< Захарія 8 >

1 І було мені слово Господнє таке:
Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
2 „Так говорить Господь Саваот: За́здрю Я за Сіон великою за́здрістю, і великою ревністю Я за́здрю за нього.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
3 Так говорить Господь: Вернуся Я до Сіону, і буду пробува́ти в сере́дині Єрусалиму, і буде зватися Єрусалим „Містом Правди“, а гора Господа Саваота — „горою святою“.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
4 Так говорить Госпо́дь Савао́т: Ще бу́дуть сидіти на єрусалимських майда́нах діди́ та баби́, і кожен з па́лицею в своїй руці через довгий вік.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
5 А міські́ майда́ни будуть перепо́внені хло́пцями та дівча́тами, що будуть ба́витися на майда́нах його.
Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
6 Так говорить Господь Саваот: Коли дивне це в оча́х останку наро́ду цього́ за цих днів, чи ж воно буде дивне в оча́х Моїх? промовляє Госпо́дь Савао́т.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
7 Так говорить Господь Саваот: Ото Я спасу́ Свій наро́д із схі́днього кра́ю та з кра́ю за́ходу сонця.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
8 І спрова́джу Я їх, і вони будуть пробува́ти в сере́дині Єрусалиму, і стануть наро́дом Моїм, а Я стану їм Богом у правді та в праведності.
Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
9 Так говорить Госпо́дь Савао́т: Нехай стануть сильними ваші руки, ви, що слухаєте цими днями слова́ ці з уст пророків, що були в день закла́дин дому Господа Саваота, храму, щоб був побудо́ваний.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
10 Бо перед цими днями не було́ нагоро́ди для люди́ни, ані нагоро́ди для худоби, і для того, хто вихо́див, і для того, хто вхо́див не було́ споко́ю від ворога, і пускав Я всіх людей одно́го проти о́дного.
Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
11 Тому́ Я тепер для останку оцьо́го наро́ду не бу́ду такий, як за тих давніх днів, промовляє Господь Саваот.
Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 Бо буде насіння миру: виноград дасть свій плід, а земля урожай свій подасть, а небо дасть ро́су свою, і вчиню Я, що решта оцьо́го наро́ду це все пося́де.
“Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
13 І станеться, як були ви прокля́ттям серед наро́дів, доме Юдин та доме Ізраїлів, так Я вас спасу́, і ви станете благослове́нням. Не бійтесь, — хай зміцні́ють ваші ру́ки!
Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
14 Бо так промовляє Госпо́дь Савао́т: Як Я ду́мав зробити вам зле, коли ваші батьки прогнівля́ли Мене, — промовляє Господь Саваот, — і не жа́лував Я,
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
15 так зно́ву заду́мав Я днями оци́ми вчинити добро Єрусалимові та Юдиному до́мові. Не бійтесь!
kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
16 Оце речі, які бу́дете робити: Говоріть правду один о́дному, правду та суд миру судіть у ваших брамах.
Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
17 І не ду́майте зла в своїм серці один проти о́дного, і не любіть неправдивої прися́ги, бо це все оте, що знена́видив Я, промовляє Господь.“
kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
18 І було мені слово Господнє таке:
Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
19 „Так говорить Господь Саваот: Піст четвертого, і піст п'ятого, і піст сьомого, і піст десятого місяця стане для Юдиного дому на радість і на втіху, та на веселі свя́та, але правду та мир любіте!
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
20 Так говорить Господь Саваот: Ще при́йдуть наро́ди та мешканці числе́нних міст.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
21 І при́йдуть ме́шканці одного міста до другого, кажучи: Ходімо, ходімо вблага́ти Господа, шукати Господа Саваота! Піду́ також я.
mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
22 І поприхо́дять числе́нні наро́ди та сильні люди шукати Господа Саваота в Єрусалимі, і блага́ти Господа.
Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
23 Так говорить Господь Саваот: І станеться тими днями, що схо́плять десять мужів з усіх язи́ків тих наро́дів, і схо́плять за по́лу юдея, говорячи: Ходімо з вами, бо ми чули: Бог з вами!“
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”

< Захарія 8 >