< До римлян 8 >
1 Тож немає тепер жодного о́суду тим, хто ходить у Христі Ісусі не за тілом, а за Духом,
Saboda haka babu kayarwa yanzu ga wadanda ke cikin Almasihu Yesu.
2 бо зако́н Духа життя в Христі Ісусі визволив мене від зако́ну гріха й смерти.
Domin ka'idar ruhun rai a cikin Almasihu Yesu ta maishe mu 'yanttatu daga ka'idar zunubi da mutuwa.
3 Бо що було неможливе для Закону, у чо́му був він безсилий тілом, — Бог послав Сина Свого в подобі гріховного тіла, і за гріх осудив гріх у тілі,
Saboda abin da shari'a bata iya aikatawa ba domin kasawa ta wurin jiki, Allah ya yi. Ya aiko da dansa a kamanin jiki mai zunubi domin ya zama hadaya domin zunubi, sai ya yi Allah wadai da zunubi a cikin jiki.
4 щоб ви́коналось ви́правдання Закону на нас, що ходимо не за тілом, а за Духом.
Ya yi haka domin bukatar shari'a ta sami cika a cikinmu, mu da muke tafe ba ta gwargwadon jiki ba, amma ta gwargwadon ruhaniya.
5 Бо ті, хто ходить за тілом, ду́мають про тілесне, а хто за Духом — про духовне.
Wadanda ke rayuwa gwargwadon jiki sukan lura da al'amuran jiki, amma su da ke rayuwa a gwargwadon Ruhu sukan mai da hankali ga al'amuran Ruhu.
6 Бо думка тілесна — то смерть, а думка духовна — життя та мир,
To kwallafa rai ga jiki mutuwa ce, amma kwallafa rai ga Ruhu rai ne da salama.
7 думка бо тілесна — ворожне́ча на Бога, бо не ко́риться Законові Божому, та й не може.
Haka yake domin kwallafa rai ga jiki gaba yake da Allah, gama baya biyyaya ga shari'ar Allah, balle ma ya iya.
8 І ті, хто хо́дить за тілом, не можуть догодити Богові.
Wadanda ke a jiki ba su iya faranta wa Allah zuciya.
9 А ви не в тілі, але в Дусі, бо Дух Божий живе в вас. А коли хто не має Христового Духа, той не Його.
Duk da haka, ba ku cikin jiki amma a cikin Ruhu, idan gaskiya ne, Ruhun Allah na rayuwa cikinku. Amma idan wani ba shi da Ruhun Almasihu, shi ba na sa bane.
10 А коли Христос у вас, то хоч тіло мертве через гріх, але дух живий через праведність.
In Almasihu na cikinka, jikin ka fa matacce ne ga zunubi, amma ruhu na rayuwa bisa ga adalci.
11 А коли живе в вас Дух Того, Хто воскресив Ісуса з мертвих, то Той, хто підняв Христа з мертвих, ожи́вить і смертельні тіла ваші через Свого Духа, що живе в вас.
Idan Ruhun wanda ya tada Yesu daga matattu na raye a cikinku, to shi wanda ya tada Almasihu da ga matattu za ya bada rai ga jikinku masu matuwa ta wurin Ruhunsa, da ke rayuwa a cikin ku.
12 Тому́ то, браття, ми не боржники́ тіла, щоб жити за тілом;
To, 'yan' uwa, muna da hakki amma ba bisa jiki ba, da za mu yi rayuwa bisa ga dabi'ar jiki.
13 бо коли живе́те за тілом, то маєте вмерти, а коли Духом умертвля́єте тілесні вчинки, то бу́дете жити.
Gama idan kun yi rayuwa gwargwadon jiki, za ku mutu kenan, amma idan ta wurin Ruhu ku ka kashe ayyukan jiki, za ku rayu.
14 Бо всі, хто водиться Духом Божим, вони сини Божі;
Gama duk wadanda Ruhun Allah ke bishe su, su 'ya 'yan Allah ne.
15 бо не взяли́ ви духа неволі знов на страх, але взяли ви Духа сині́вства, що через Нього кличемо: „Авва, Отче!“
Gama ba ku karbi ruhun bauta da ke sa tsoro ba. Maimakon haka, kun karbi ruhun diyanci, ta wurinsa muke tadda murya muna kira, “Abba, Uba!”
16 Сам Цей Дух сві́дчить ра́зом із духом нашим, що ми — діти Божі.
kansa na bada shaida tare da namu ruhun cewa mu 'ya'yan Allah ne.
17 А коли діти, то й спадкоємці, спадкоємці ж Божі, а співспадкоємці Христові, коли тільки ра́зом із Ним ми терпимо́, щоб разом із Ним і просла́витись.
Idan mu 'ya'ya ne, ai mu magada ne kenan, magadan Allah. Kuma mu magada ne tare da Almasihu, hakika idan mun sha wahala tare da shi za a kuma daukaka mu tare da shi.
18 Бо я ду́маю, що страждання тепе́рішнього ча́су нічого не варті супроти тієї слави, що має з'явитися в нас.
Gama na yi la'akari cewa wahalonin zamanin nan ba su isa a kwatanta su da daukakar da za'a bayyana mana ba.
19 Бо чека́ння створі́ння очікує з'я́влення синів Божих,
Saboda yadda halitta ke marmarin bayyanuwar 'ya'yan Allah.
20 бо створі́ння покорилось марно́ті не добровільно, але через того, хто скори́в його, в надії,
Gama an kaskantar da halitta ga banza, ba da nufin ta ba, amma na shi wanda ya kaskantar da ita. Ta na cikin tabbacin alkawarin.
21 що й саме створіння ви́зволиться від неволі тління на волю слави синів Божих.
Cewa halitta kanta za ta kubuta daga bautar rubewa, kuma za a kawo ta zuwa ga 'yantarwa na yabon daukakar 'ya'yan Allah.
22 Бо знаємо, що все створі́ння ра́зом зідхає й ра́зом мучиться аж досі.
Gama mun sani dukan halitta na nishi da zafin nakuda tare har ya zuwa yanzu.
23 Але не тільки воно, але й ми самі, маючи зача́ток Духа, і ми самі в собі зідхаємо, очікуючи синівства, відкуплення нашого тіла.
Ba haka kadai ba, amma ko mu kanmu, da ke nunar farko na Ruhu—mu kanmu muna nishi acikin mu, muna jiran diyancinmu, wato ceton jikinmu kenan.
24 Надією бо ми спасли́ся. Надія ж, коли бачить, не є надія, бо хто що́ бачить, чому б того й наді́явся?
Gama ta wanan hakikancewa aka cece mu. Amma dai abin da muke da tabbacin zai faru ba mu gan shi ba tukuna, domin wanene wa ke begen tabbatacce abin da yake gani?
25 А коли сподіва́ємось, чого не бачимо, то очікуємо того з терпеливістю.
Amma idan muna da tabbacin abin da ba mu gani ba tukuna, to sai mu jjira shi da hakuri.
26 Так само ж і Дух допомагає нам у наших не́мочах; бо ми не знаємо, про що маємо молитись, як належить, але Сам Дух заступається за нас невимо́вними зідха́ннями.
Hakanan, Ruhu kuma ke taimako a kasawarmu. Gama ba mu da san yadda zamu yi addu'a ba, amma Ruhu kansa na roko a madadinmu da nishe-nishen da ba'a iya ambatawa.
27 А Той, Хто досліджує серця́, знає, яка думка Духа, бо з волі Божої заступається за святих.
Shi da ke bidar zuciya yana sane da tunanin Ruhu, domin yana roko a madadin masu badagaskiya ta wurin nufin Allah.
28 І знаємо, що тим, хто любить Бога, хто покликаний Його постановою, усе допомагає на добре.
Mun san cewa ga wadanda ke kaunar Allah, yakan aikata dukan al'amura domin su zuwa ga alheri, ga duk wadanda aka kira bisa ga nufinsa. Dukan abubuwa sukan zama alheri.
29 Бо кого Він передба́чив, тих і призна́чив, щоб були подібні до о́бразу Сина Його, щоб Він був перворі́дним поміж багатьма́ братами.
Saboda wadanda ya sani tuntuni su ne ya kardara su zama da kamanin dansa, domin ya zama dan fari a cikin 'yan'uwa masu yawa.
30 А кого Він призначив, тих і покликав, а кого покликав, тих і ви́правдав, а кого ви́правдав, тих і просла́вив.
Su da ya kaddara, ya kiraye su. Wadanda ya kira, su ya kubutar. Su da ya kubutar, sune kuma ya daukaka.
31 Що ж скажем на це? Коли за нас Бог, то хто проти нас?
Me zamu ce game da wadannan al'amura? Idan Allah na tare da mu, wake gaba da mu?
32 Той же, Хто Сина Свого не пожалів, але видав Його за всіх нас, — як же не дав би Він нам із Ним і всього?
Shi da baya hana dansa ba, amma ya bada shi a madadinmu dukka, me zai hana shi bamu dukkan abubuwa a yalwace tare da shi?
33 Хто оска́ржувати буде Божих вибранців? Бог Той, що виправдує.
Wa zaya kawo wata tuhuma ga zababbu na Allah? Allah ne ke “yantarwa.
34 Хто ж той, що засу́джує? Христос Ісус є Той, що вмер, надто й воскрес, — Він право́руч Бога, і Він і заступається за нас.
Wanene ke hukumtawa? Almasihu ne da ya mutu sabili da mu har ma fiye da haka, shi wanda kuma aka tasar. Yana mulki tare da Allah a wuri mai daukaka, shi ne kuma ya ke roko sabili da mu.
35 Хто нас розлучить від любови Христової? Чи недоля, чи утиск, чи переслі́дування, чи голод, чи нагота́, чи небезпека, чи меч?
Wa za ya raba mu da kaunar Allah? Kunci, ko bacin rai, ko tsanani, ko yunwa, ko tsiraci, ko hadari, ko takobi?
36 Як написано: „За Тебе нас цілий день умертвля́ють, нас уважають за овець, прирече́них на зако́лення“.
Kamar yadda aka rubuta, “Saboda kai ake kisanmu dukkan yini. An mai da mu kamar tumaki yanka.”
37 Але в цьому всьому ми перемагаємо Тим, Хто нас полюбив.
A dukan al'amuran nan mun fi karfi a ce da mu masu nasara ta wurin shi da ke kaunar mu.
38 Бо я пересві́дчився, що ні смерть, ні життя, ні анголи́, ні вла́ди, ні тепе́рішнє, ні майбу́тнє, ні сили,
Gama na tabata cewa ko mutuwa, ko rai, ko mala'iku, ko mulkoki, ko al'amuran yanzu, ko al'amura masu zuwa, ko iko,
39 ні вишина́, ні глибина́, ані інше яке створіння не зможе відлучити нас від любови Божої, яка в Христі Ісусі, Господі нашім!
ko tsawo, ko zurfi, kai ko wace irin halitta, ba su isa su raba mu da kaunar Allah, da ke a cikin Almasihu Yesu Ubangijin mu ba.