< До римлян 4 >

1 Що ж, скажемо, знайшов Авраа́м, наш отець за тілом?
To, me za mu ce Ibrahim kakan kakanninmu ya gani game da wannan batu?
2 Бо коли Авраам ви́правдався діла́ми, то він має похвалу, та не в Бога.
In fa da gaske ne Ibrahim ya sami kuɓuta ta wurin ayyuka, yana da abin da zai yin taƙama da shi ke nan, amma ba a gaban Allah ba.
3 Що бо Писа́ння говорить? „Увірував Авраам Богові, і це йому залічено в праведність“.
Me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
4 А заплата викона́вцеві не рахується з милости, але з обов'язку.
To, sa’ad da mutum ya yi aiki, ba a lissafta ladan aikinsa a matsayin kyauta, sai dai a matsayin hakkinsa.
5 А тому́, хто не виконує, але вірує в Того, Хто виправдує нечестивого, віра його порахується в праведність.
Amma fa, game da mutumin da ba ya aiki sai dai dogara ga Allah wanda yake kuɓutar da masu mugunta, akan lissafta bangaskiyarsa a matsayin adalci ne.
6 Як і Давид називає блаженною люди́ну, якій рахує Бог праведність без діл:
Dawuda ya faɗi haka sa’ad da ya yi magana game da albarkar da aka yi wa mutumin da Allah ya lissafta adalci a gare shi, ba don yă yi ayyuka ba.
7 „Блаженні, кому прощені беззаконня, і кому прикриті гріхи.
“Masu albarka ne waɗanda aka gafarta laifofinsu, waɗanda aka kuma rufe zunubansu.
8 Блаженна людина, якій Господь не порахує гріха́!“
Mai albarka ne mutumin da Ubangiji ba zai taɓa lissafta zunubansa ba.”
9 Чи ж це блаже́нство з обрізання чи з необрізання? Бо говоримо, що „віра залічена Авраамові в праведність“.
Shin, wannan albarkar a kan masu kaciya ne kawai, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Mun sha faɗi cewa an lissafta bangaskiyar Ibrahim adalci ne a gare shi.
10 Як же залічена? Як був в обрізанні, чи в необрізанні? Не в обрізанні, але в необрізанні!
A kan wane hali ne aka lissafta masa? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa kafin kaciyar? Ba bayan an yi masa kaciya ba ne, amma kafin a yi masa kaciya!
11 І прийняв він ознаку обрізання, — печать праведности через віру, що її в необрізанні мав, щоб йому бути отцем усіх віруючих, хоч були необрізані, щоб і їм залічено праведність,
Ya kuma karɓi alamar kaciya, hatimin adalcin da yake da shi ta wurin bangaskiya tun yana marar kaciya. Saboda haka fa, ya zama mahaifin dukan waɗanda suka gaskata domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba.
12 і отцем обрізаних, не тільки тих, хто з обрізання, але й тих, хто ходить по слідах віри, що її в необрізанні мав наш отець Авраам.
Ya kuma zama mahaifin masu kaciya waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba amma har ma suna bin gurbin bangaskiyar da mahaifinmu Ibrahim yake da ita kafin aka yi masa kaciya.
13 Бо обі́тницю Авраамові чи його насінню, що бути йому спадкоємцем світу, дано не Зако́ном, але праведністю віри.
Ba ta wurin doka ce Ibrahim da zuriyarsa suka sami alkawarin cewa zai zama magājin duniya ba, amma sai dai ta wurin adalcin da yake zuwa ta wurin bangaskiya.
14 Бо коли спадкоємці ті, хто з Зако́ну, то спорожніла віра й зні́вечилась обі́тниця.
Gama da a ce masu kiyaye doka ne magāda, ai, da bangaskiya ba ta da amfani, alkawarin kuma ya zama banza,
15 Бо Зако́н чинить гнів; де ж немає Закону, немає й пере́ступу.
domin doka tana jawo fushi ne. Kuma inda babu doka babu keta umarni ke nan.
16 Через це з віри, щоб було з милости, щоб обі́тниця певна була всім нащадкам, не тільки тому́, хто з Закону, але й тому́, хто з віри Авраама, що отець усім нам,
Saboda haka, alkawari yakan zo ta wurin bangaskiya ne, domin yă zama ta wurin alheri, don a tabbatar wa dukan zuriyar Ibrahim ba kawai ga waɗanda suke na doka ba amma har ma ga waɗanda suke na bangaskiyar Ibrahim. Shi ne kuwa mahaifinmu duka.
17 як написано: „Отцем багатьох наро́дів Я поставив тебе, “— перед Богом, Якому він вірив, Який оживляє мертвих і кличе неіснуюче, як існуюче.
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na mai da kai uban al’ummai masu yawa.” Shi ubanmu ne a gaban Allah, wanda a cikinsa ya gaskata, Allahn da yake ba da rai ga matattu, yake kuma kiran abubuwan da ba su kasance ba su zama kamar sun kasance.
18 Він — проти надії — увірував у надії, що стане батьком багатьох народів, за сказаним: „Таке числе́нне буде насіння твоє!“
Saɓanin dukan bege, Ibrahim cikin bege ya gaskata, haka kuwa ya zama uban al’ummai masu yawa, kamar yadda aka riga aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
19 І не знеміг він у вірі, і не вважав свого тіла за вже омертвіле, бувши майже сторічним, ні утро́би Сариної за змертвілу,
Ba tare da ya bar bangaskiyarsa ta yi rauni ba, ya fuskanci gaskiyan nan mai cewa jikinsa mai tsufa matacce ne, da yake yana da shekara wajen ɗari, mahaifar Saratu kuma matacciya ce.
20 і не мав сумніву в обі́тницю Божу через недові́рство, але зміцни́вся в вірі, і віддав славу Богові,
Duk da haka bai yi shakka ta wurin rashin bangaskiya game da alkawarin Allah ba, sai ma ya ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa, ya kuma ɗaukaka Allah,
21 і був зовсім певний, що Він має силу й виконати те, що обіцяв.
yana kuma da cikakken tabbaci cewa Allah yana da iko yă cika abin da ya yi alkawari.
22 Тому й „залічено це йому в праведність“.
Shi ya sa, “aka lissafta adalci a gare shi.”
23 Та не написано за нього одно́го, що залічено йому,
Kalmomin nan, “aka lissafta a gare shi” ba a rubuta su saboda shi kaɗai ba ne,
24 а за нас, — залі́читься й нам, що віруємо в Того, Хто воскресив із мертвих Ісуса, Господа нашого,
amma saboda mu ma, mu da Allah zai lissafta adalci, mu da muka ba da gaskiya gare shi da ya tashe Yesu Ubangijinmu daga matattu.
25 що був виданий за наші гріхи, і воскрес для ви́правдання нашого.
An miƙa shi ga mutuwa saboda zunubanmu, aka kuma tashe shi zuwa rai saboda Allah zai same mu marasa laifi.

< До римлян 4 >