< До римлян 3 >
1 Отож, що́ має більшого юдей, або яка ко́ристь від обрі́зання?
To ina fifikon da bayahude yake dashi? Kuma ina ribar kaciya?
2 Багато, на всякий спосіб, а насамперед, що їм довірені були́ Слова́ Божі.
Akwai muhimmancinsu ta kowacce hanya. Tun farko dai, yahudawa ne aka dankawa wahayi daga Allah.
3 Бо що ж, що не вірували деякі? Чи ж їхнє недовірство знищить вірність Божу?
Idan wasu yahudawa basu bada gaskiya ba fa? Rashin bangaskiyarsu zai hana amincin Allah aiki?
4 Зо́всім ні! Бож Бог правдивий, а кожна люди́на неправдива, як написано: „Щоб був Ти ви́правданий у словах Своїх, і переміг, коли будеш судитися“.
Bazai taba zama haka ba. Maimakon haka, bari Allah ya zama mai gaskiya, ko da kowanne mutum makaryaci ne. Kamar yadda aka rubuta, “Domin a nuna kai mai adalci cikin maganganunka, kuma kayi nasara a lokacin da aka kawo ka gaban shari'a.”
5 А коли наша неправедність виставляє праведність Божу, то що скажемо? Чи ж Бог несправедгливий, коли гнів виявляє? Говорю́ по-лю́дському.
Amma idan rashin adalcinmu ya nuna adalcin Allah, to me zamu ce? Allah ba marar adalci ba ne, wanda ke aiwatar da fushinsa, ko kuwa? Ina magana bisa ga tunanin mutuntaka.
6 Зо́всім ні! Бож як Бог судитиме світ?
Bazai taba zama haka ba. Domin idan haka ne ta yaya Allah zai shar'anta duniya?
7 Бо коли Божа правда через мою неправду збі́льшилась на славу Йому, пощо судити ще й мене, як грішника?
Amma idan gaskiyar Allah ta wurin karyata ta habaka yabonsa, To me yasa ake shar'anta ni a matsayin mai zunubi?
8 І чи не так, як нас лають, і як деякі гово́рять, ніби ми кажемо: „Робімо зле, щоб вийшло добре?“Справедливий о́суд на таких!
To me zai hana ace kamar yadda ake fadin zancen karya a kanmu, wasu kuma sun dauka cewa mun fadi hakan, “Bari muyi mugunta, domin nagarta tazo?” Hukuncin su halal ne.
9 То що ж? Маємо перевагу? Анітро́хи! Бож ми перед тим довели́, що юдеї й ге́ллени — усі під гріхом,
To me kenan? Zamu ba kanmu hujja ne? ko kadan. Domin mun riga munyi zargin yahudawa da hellinawa, da cewar dukkansu, suna karkashin zunubi.
10 як написано: „Нема праведного ані о́дного;
Kamar yadda aka rubuta, babu wani mai adalci, babu ko daya.
11 нема, хто розумів би; немає, хто Бога шукав би, —
Babu wani mai fahimta. Babu wani mai neman Allah.
12 усі повідступа́ли, ра́зом стали непотрібні, нема доброчинця, нема ні одно́го!
Dukansu sun kauce hanya, dukansu gaba daya sun zama marasa amfani. Babu mai aikin nagarta, a'a, babu ko da guda daya.
13 Гріб відкритий — їхнє горло, язиком своїм кажуть неправду, отрута зміїна на їхніх губа́х,
Makogwaronsu a bude yake kamar kabari. Harsunansu na dauke da cuta. Dafin macizai na karkashin lebunansu.
14 уста́ їхні повні прокляття й гірко́ти!
Bakunansu cike suke da la'ana da daci.
15 Швидкі їхні ноги, щоб кров проливати,
Sawayensu na saurin zuwa zubar da jini.
16 руїна та злидні на їхніх дорогах,
Tafarkinsu wahala ce da lalacewa.
17 а дороги миру вони не пізнали!
Wadannan mutane basu san hanyar salama ba.
18 Нема страху Божого перед очима їхніми“.
Babu tsoron Allah a idanunsu.”
19 А ми знаємо, що скільки гово́рить Зако́н, він говорить до тих, хто під Зако́ном, щоб замкнути всякі уста́, і щоб став увесь світ винний Богові.
To mun san dai duk abin da shari'a tace, shari'a na magana ne da wadanda ke karkashinta, domin a rufe kowanne baki, domin dukan duniya ta bada amsa a gaban Allah.
20 Бо жодне тіло ділами Зако́ну не ви́правдається перед Ним, — Зако́ном бо гріх пізнається.
Domin a gabansa babu wanda zai barata ta wurin ayukan shari'a. Domin ta wurin shari'a ne sanin zunubi yazo.
21 А тепер, без Зако́ну, праведність Божа з'вилась, про яку свідчать Зако́н і Пророки.
Amma yanzu ba tare da shari'a ba an bayyana sanin adalcin Allah, wanda shari'a da annabawa suke shaidawa.
22 А Божа праведність через віру в Ісуса Христа в усіх і на всіх, хто вірує, бо різниці немає,
Wato, adalcin Allah ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ga dukkan wadanda ke bada gaskiya. Domin babu bambanci:
23 бо всі згрішили, і позбавлені Божої слави,
Domin duk sun yi zunubi sun kuma kasa kaiwa ga darajar Allah,
24 але дарма́ виправдуються Його благода́ттю, через відку́плення, що в Ісусі Христі,
Da alherinsa an baratar da mu ta wurin fansar dake cikin Yesu Almasihu.
25 що Його Бог дав у жертву прими́рення в крові Його через віру, щоб виявити Свою праведність через відпу́щення давніше вчинених гріхів,
Amma Allah ya bayar da Yesu Almasihu wanda yake hadayar fansa ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya mika Almasihu a matsayin tabbacin hukuncinsa, sabo da kuma ketarewar zunubanmu na baya
26 за довготерпі́ння Божого, щоб виявити Свою праведність за теперішнього ча́су, щоб бути Йому праведним, і виправдувати того, хто вірує в Ісуса.
cikin hakurinsa. Duk wannan ya faru ne domin a bayyana adalcinsa cikin wannan zamani, domin ya tabbatar da kansa mai hukunci, kuma ya nuna shine mai baratar da kowa saboda bangaskiya cikin Yesu.
27 Тож де похвальба́? Виключена. Яким зако́ном? Законом діл? Ні, але зако́ном віри.
To ina fahariya? An fitar da ita. A kan wane dalilin? Don ayyuka? A'a, amma ta dalilin bangaskiya.
28 Отож, ми визнаємо, що люди́на виправдується вірою, — без діл Зако́ну.
Domin wannan muka kammala cewar ana baratar da mutum ta wurin bangaskiya ba tare da ayyukan shari'a ba.
29 Хіба ж Бог тільки для юдеїв, а не й для поган? Так, і для поган,
Ko kuwa Allah Allahn yahudawa ne kadai? Shi ba Allahn al'ummai bane? I, na al'ummai ne kuma.
30 бо є один тільки Бог, що ви́правдає обрізання з віри й необрізання через віру.
Idan dai lallai Allah daya ne, zai baratar da mai kaciya ta wurin bangaskiya, da marar kaciya kuma ta wurin bangaskiya.
31 Тож чи не нищимо ми Зако́на вірою? Зо́всім ні, — але зміцнюємо Зако́на.
Mun kawar da shari'a kenan ta wurin bangaskiya? ba zai taba kasancewa haka ba. Maimako ma, muna inganta shari'a kenan.