< До римлян 14 >

1 Слабо́го в вірі приймайте, але не для суперечок про погляди.
Ku karbi duk wanda yake da rarraunar bangaskiya, ba tare da sukar ra'ayinsa ba.
2 Один бо вірує, що можна їсти все, а не́мічний споживає ярину́.
Wani yana da bangaskiyar yaci komai, wani wanda yake da rauni yakanci ganye ne kawai.
3 Хто їсть, нехай не погорджує тим, хто не їсть. А хто не їсть, нехай не осуджує того, хто їсть, — Бог бо прийняв його.
Kada wanda yake cin komai ya raina wanda baya cin kowanne abu. Kada kuma wanda baya cin kowanne abu ya shara'anta sauran da suke cin komai. Saboda Allah ya karbe shi.
4 Ти хто такий, що судиш чужого раба? Він для пана свого стоїть або падає; але він усто́їть, бо має Бог силу поставити його.
Kai wanene, kai wanene da kake ganin laifin bawan wani? Tsayawarsa ko faduwarsa ai hakin maigidansa ne, amma Ubangiji yana da ikon tsai da shi.
5 Один вирі́знює день від дня, інший же про кожен день судить одна́ково. Нехай кожен за власною думкою тримається свого переко́нання.
Wani yakan daukaka wata rana fiye da sauran. Wani kuma yana daukan ranakun daidai. Kowa ya zauna a cikin hakakkewa akan ra'ayinsa.
6 Хто вважає на день, — для Господа вважає, а хто не вважає на день, — для Господа не вважає. Хто їсть, — для Господа їсть, бо дякує Богові. А хто не їсть, — для Господа не їсть, і дякує Богові.
Shi wanda ya kula da wata rana, ya kula da ita don Ubangiji. Kuma wanda yaci, yaci ne domin Ubangiji, domin yana yi wa Allah godiya. Shi wanda bai ci ba, yaki ci ne domin Ubangiji. Shima yana yi wa Allah godiya.
7 Бо ніхто з нас не живе сам для себе, і не вмирає ніхто сам для себе.
Domin babu wanda yake rayuwa don kansa a cikinmu, kuma babu mai mutuwa don kansa.
8 Бо коли живемо́ — для Господа живемо́, і коли вмира́ємо — для Господа вмираємо. І чи живемо́, чи вмира́ємо — ми Господні!
Domin in muna raye, muna raye don Ubangiji. Kuma in mun mutu, mun mutu ne don Ubangiji. Ashe, ko muna raye, ko a mace mu na Ubangiji ne.
9 Бо Христос на те й умер, і ожив, щоб панувати і над мертвими, і над живими.
Domin wannan dalilin Almasihu ya mutu ya kuma tashi, saboda ya zama Ubangiji ga matattu da rayayyu.
10 А ти на́що осуджуєш брата свого́? Чи чого ти пого́рджуєш братом своїм? Бо всі станемо перед судним престолом Божим.
Amma ku don me kuke shara'anta yan'uwanku? kai kuma don me kake raina dan'uwanka? Dukan mu zamu tsaya gaban kursiyin shari'ar Allah.
11 Бо написано: „Я живу, каже Госпо́дь, і схи́литься кожне коліно передо Мною, і ви́знає Бога кожен язик!“
Domin a rubuce yake, “Na rantse, “inji Ubangiji”, kowacce gwiwa zata rusuna mani, kowanne harshe kuwa zai yabi Allah.”
12 Тому кожен із нас сам за себе дасть відповідь Богові.
Domin kowannenmu zai fadi abin da shi yayi da bakinsa a gaban Allah.
13 Отож, не будемо більше осуджувати один о́дного, але краще судіть про те, щоб не давати братові спотика́ння та спокуси.
Saboda da haka kada muyi wa juna shari'a, amma maimakon haka ku dauki wannan kudduri, don kada kowa ya zama sanadin tuntunbe ko faduwa ga dan'uwansa.
14 Я знаю, і пересвідчений у Господі Ісусі, що нема нічо́го нечистого в само́му собі; тільки коли хто вважає що за нечисте, тому́ воно нечисте.
Na sani na kuma tabbata tsakani na da Ubangiji Yesu, ba abin da yake mara tsarki ga asalinsa. Sai dai ga wanda ya dauke shi marar tsarki ne yake zama marar tsarki.
15 Коли ж через поживу сумує твій брат, то вже не за любов'ю пово́дишся ти, — не губи своєю поживою того́, за кого Христос був умер.
Idan har abincinka na cutar da dan'uwanka, ba ka tafiya cikin kauna. Kada ka lalata wanda Yesu ya mutu domin sa da abincinka.
16 Нехай ваше добре не зневажа́ється.
Saboda haka, kada abubuwan da aka dauka kyawawa su zama abin zargi ga wadansu.
17 Бо Царство Боже не пожи́ва й питво́, але праведність, і мир, і радість у Дусі Святім.
Saboda mulkin Allah ba maganar ci da sha ba ne, amma game da adalci ne, salama, da farin ciki a cikin Ruhu Mai Tsarki.
18 Хто цим служить Христові, той Богові милий і шано́ваний поміж людьми́.
Domin wanda yake bautar Almasihu a wannan hanya, karbabbe ne ga Allah, kuma jama'a sun yarda da shi.
19 Отож, пильнуймо про мир, та про те, що на збудува́ння один о́дного!
Don haka, mu nemi abubuwa na salama da abubuwan da zasu gina juna.
20 Не руйнуй діла Божого ради поживи, — усе бо чисте, але зле люди́ні, що їсть на спотика́ння.
Kada ku lalata aikin Allah don abinci. Komai yana da tsarki, amma kaiton mutumin da yake cin abin da zai sa shi ya fadi.
21 Добре не їсти м'яса, ані пити вина, ані робити такого, від чого брат твій гірши́ться, або споку́шується, або слабне.
Bashi da kyau a ci nama ko a sha ruwan inabi, ko duk abin da zai jawo faduwar dan'uwanka.
22 Ти маєш віру? Май її сам про себе перед Богом. Блаженний той, хто не осуджує самого себе за те, про що випробо́вується!
Wannan bangaskiyar da kuke da ita, ku adana ta tsakaninku da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa bata da laifi akan abin da hankalinsa ya ga daidai ne.
23 А хто має сумнів, коли їсть, буде осу́джений, бо не робить із віри, а що не від віри, те гріх.
Duk wanda yayi shakka amma kuma yaci, ya sani yayi laifi kenan, domin ba tare da bangaskiya bane. Duk abin da ba na bangaskya bane zunubi ne.

< До римлян 14 >