< Неемія 10 >

1 А між тих, що поклали печа́тки, були: намісник Неемія, син Хахаліїн, і Цідкійя,
Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
2 Серая, Азарія, Єремія,
da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
3 Пашхур, Амарія, Малкійя,
da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
4 Хаттуш, Шеванія, Маллух,
da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
5 Харім, Меремот, Овадія,
da Harim, da Meremot, da Obadiya,
6 Даніїл, Ґіннетон, Барух,
da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
7 Мешуллам, Авійя, Мійямін,
da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
8 Маазія, Білґай, Шемая, — оце священики.
da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
9 А Леви́ти: Ісус, син Азаніїн, Біннуй, з Хенададових синів, Кадміїл.
Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
10 А їхні брати: Шеванія, Годійя, Келіта, Пелая, Ханан,
’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
11 Міха, Рехов, Хашавія,
da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
12 Заккур, Шеревія, Шеванія,
da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
13 Годійя, Бані, Беніну.
da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
14 Го́лови наро́ду: Пар'ош, Пахат-Моав, Елам, Затту, Бані,
Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
15 Бунні, Аз'дад, Бевай,
da Bunni, da Azgad, da Bebai,
16 Адонійя, Біґвай, Адін,
da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
17 Атер, Хізкійя, Аззур,
da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
18 Годійя, Хашум, Бецай,
da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
19 Харіф, Анатот, Невай,
da Harif, da Anatot, da Nebai,
20 Маґпіяш, Мешуллам, Хезір,
da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
21 Мешезав'їл, Садок, Яддуя,
da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
22 Пелатія, Ханан, Аная,
da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
23 Осі́я, Хананія, Хашшув,
da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
24 Галлохеш, Пілха, Шовек,
da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
25 Рехум, Хашавна, Маасея,
da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
26 і Ахійя, Ханан, Анан,
da Ahiya, da Hanan, da Anan,
27 Маллух, Харім, Баана.
da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
28 І решта наро́ду, священики, Левити, придве́рні, співаки́, храмові́ підда́нці, і кожен, відділений від наро́дів кра́ю до Божого Зако́ну, їхні жінки́, їхні сини́, та їхні до́чки, кожен знаю́чий та розуміючий,
“Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
29 зміцня́ють прися́гу при браттях своїх, при своїх шляхе́тних, і вступили в клятву та прися́гу, щоб ходити в Божому Зако́ні, що був да́ний через Мойсея, Божого раба, і щоб дотри́муватися, і щоб вико́нувати всі заповіді Господа, нашого Бога, і права Його, і постано́ви Його,
dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
30 і що не дамо́ наших синів наро́дам кра́ю, а їхніх дочо́к не ві́зьмемо для наших синів.
“Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
31 А від наро́дів цього Кра́ю, що спрова́джують това́ри та всяке збі́жжя в день субо́тній на про́даж, не ві́зьмемо від них у суботу та в святі дні, і сьо́мого року понеха́ємо землю та всякого роду борги́.
“Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
32 І поставили ми собі за обов'я́зок, щоб давати нам третину шекля в рік на службу дому нашого Бога,
“Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
33 на хліб показни́й, і на пості́йний дар, і на пості́йне цілопа́лення, на суботи, на молодики́, на свята, і на освячені речі, і на же́ртви за гріх на оку́плення за Ізраїля, і на всяку працю дому нашого Бога.
Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
34 І кинули ми жеребки́ про пожертву дров, священики, Левити та наро́д, щоб прино́сити до дому нашого Бога, за домом наших батьків, на озна́чені часи́ рік-річно, щоб палити на же́ртівнику Господа, нашого Бога, як напи́сано в Зако́ні,
“Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
35 і щоб прино́сити первопло́ди нашої землі та первопло́ди всякого пло́ду зо всякого де́рева рік-річно до Господнього до́му,
“Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
36 і перворо́джених синів наших та нашої худоби, як написано в Зако́ні, і перворо́джених худоби нашої великої та худоби нашої дрібно́ї, щоб прино́сити до дому нашого Бога до священиків, що служать у домі нашого Бога,
“Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
37 і первопоча́ток наших діж, і наші прино́шення, і плід усякого де́рева, молоде́ вино та оливу спрова́димо священикам до кімна́т дому нашого Бога, а десятину нашої землі — Левитам. А вони, Левити, будуть збирати десятину по всіх містах нашої роботи.
“Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
38 І буде священик, син Ааронів, із Левитами, коли Левити будуть збирати десятину, і Левити віднесу́ть десятину від десятини до дому нашого Бога до комір, до скарбни́ці.
Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
39 Бо до комір будуть зно́сити сини Ізраїлеві та сини Левитів прино́шення збіжжя, молодо́го вина та оливи, і там є речі святині, служачі священики, і придве́рні, і співаки́. І ми не опу́стимо дому нашого Бога!
Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”

< Неемія 10 >