< Плач Єремії 3 >

1 Я той муж, який бачив біду́ від жезла́ Його гніву, —
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Він прова́див мене й допрова́див до те́мряви, а не до світла.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Лиш на мене все зно́ву обе́ртає руку Свою́ цілий день.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Він ви́снажив тіло моє й мою шкіру, мої кості сторо́щив,
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 обгородив Він мене, і мене оточи́в гіркото́ю та му́кою,
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 у темно́ті мене посадив, мов померлих давно́.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Обгороди́в Він мене — і не ви́йду, тяжки́ми вчинив Він кайда́ни мої.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 І коли я кричу́ й голошу́, затикає Він вуха Свої на молитву мою,
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 Камінням обте́саним обгородив Він доро́ги мої, повикри́влював стежки́ мої.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Він для мене ведме́дем чату́ючим став, немов лев той у схо́вищі!
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 Поплутав доро́ги мої та розша́рпав мене́, учинив Він мене опусто́шеним!
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 Натягнув Свого лука й поставив мене, наче ціль для стріли́, —
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 пустив стрі́ли до ни́рок моїх з Свого сагайдака́
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 Для всього наро́ду свого я став посміхо́виськом, глумли́вою піснею їхньою цілий день.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 Наси́тив мене гіркото́ю, мене напоїв полино́м.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 І стер мені зу́би жорство́ю, до по́пелу кинув мене,
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 і душа моя спо́кій згубила, забув я добро́.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 І сказав я: Загублена сила моя, та моє сподіва́ння на Господа.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Згадай про біду́ мою й му́ку мою, про поли́н та отру́ту, —
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 душа моя згадує безпереста́нку про це, і гнеться в мені.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Оце я нага́дую серцеві своєму, тому то я маю надію:
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Це милість Господня, що ми не поги́нули, бо не нокінчи́лось Його милосердя, —
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 нове́ воно кожного ра́нку, велика бо вірність Твоя!
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 Господь — це мій у́діл, — говорить душа моя, — тому́ я надію на Нього склада́ю!
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Господь добрий для тих, хто наді́ю на Нього кладе́, для душі, що шукає Його́!
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 Добре, коли люди́на в мовча́нні надію кладе́ на спасі́ння Господнє.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 Добре для мужа, як носить ярмо́ в своїй мо́лодості, —
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 нехай він самі́тно сидить і мовчить, як поклав Він на нього його́;
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 хай закриє він по́рохом у́ста свої, може є ще надія;
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 хай що́ку тому підставля́є, хто його б'є, своєю ганьбою наси́чується.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Бо Господь не наві́ки ж покине!
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Бо хоч Він і засму́тить кого, проте зми́лується за Своєю великою ми́лістю, —
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 бо не мучить Він з серця Свого́, і не засмучує лю́дських синів.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 Щоб топта́ти під своїми ногами всіх в'я́знів землі,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 щоб перед обличчям Всевишнього право люди́ни зігнути,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 щоб гноби́ти люди́ну у справі судо́вій його́, — оцьо́го не має на оці Госпо́дь!
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Хто то скаже — і станеться це, як Господь того не наказав?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Хіба не виходить усе з уст Всевишнього, — зле та добре?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Чого ж нарікає люди́на жива? Нехай ска́ржиться кожен на гріх свій.
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Пошукаймо доріг своїх та досліді́мо, і верні́мось до Господа!
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 підіймі́мо своє серце та руки до Бога на небі!
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 Спроневі́рились ми й неслухня́ними стали, тому́ не пробачив Ти нам,
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 закрився Ти гнівом і гнав нас, убивав, не помилував,
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 закрив Себе хмарою, щоб до Тебе молитва моя не дійшла.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Сміття́м та оги́дою нас Ти вчинив між наро́дами,
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 наші всі вороги́ пороззявля́ли на нас свого рота,
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 страх та яма на нас поприхо́дили, руїна й погибіль.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Моє око сплива́є пото́ками во́дними через нещастя дочки́ мого люду.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Виливається око моє безупи́нно, нема бо пере́рви,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 аж поки не згля́неться та не побачить Госпо́дь із небе́с, —
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 моє око вчиняє журбу́ для моєї душі через до́чок усіх мого міста.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Ло́влячи, ло́влять мене, немов птаха, мої вороги безпричи́нно,
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 життя моє в яму замкну́ли вони, і камі́ннями кинули в мене.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Пливуть мені во́ди на го́лову, я говорю́: „ Вже погу́блений я!“
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Кликав я, Господи, Йме́ння Твоє́ із найглибшої ями,
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Ти чуєш мій голос, — не захо́вуй же ву́ха Свого від зо́йку мого́, від блага́ння мого!
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Ти близьки́й того дня, коли кличу Тебе, Ти говориш: „Не бійся!“
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 За душу мою Ти змагався, о Господи, життя моє викупив Ти.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Ти бачиш, о Господи, кривду мою, — розсуди ж Ти мій суд!
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Усю їхню по́мсту ти бачиш, всі за́думи їхні на мене,
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Ти чуєш, о Господи, їхні нару́ги, всі за́думи їхні на ме́не,
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 мову повста́нців на мене та їхнє буркоті́ння на мене ввесь день.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Побач їхнє сиді́ння та їхнє встава́ння, — як за́вжди глумли́ва їхня пісня!
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Заплати їм, о Господи, згідно з чином їхніх рук!
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Подай їм темно́ту на серце, прокля́ття Твоє нехай буде на них!
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Своїм гнівом жени їх, і ви́губи їх з-під Господніх небе́с!
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Плач Єремії 3 >