< Юда 1 >
1 Юда, раб Ісуса Христа, а брат Якова, — покликаним, улю́бленим у Бозі Отці та збереженим Ісусом Христом:
Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
2 милість вам, і мир, і любов хай примно́житься!
Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
3 Улюблені, всяке дбання́ чинивши писати до вас про наше спільне спасі́ння, я признав за потрібне писати до вас, благаючи боротись за віру, раз дану святим.
Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
4 Бо крадькома́ повхо́дили деякі люди, на цей о́суд віддавна призначені, безбожні, що благода́ть нашого Бога оберта́ють у розпусту, і відкидаються єдиного Владики і Господа нашого — Ісуса Христа.
Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
5 А я хо́чу нагадати вам, що раз усе знаєте, що Госпо́дь ви́зволив людей від землі єгипетської, а згодом вигубив тих, хто не вірував.
Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
6 І анголі́в, що не зберегли початкового стану свого, але кинули жи́тло своє, Він зберіг у вічних кайда́нах під те́мрявою на суд великого дня. (aïdios )
Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios )
7 Як Содо́м і Гомо́рра та міста́ коло них, що таким самим способом чинили пере́люб та ходили за іншим тілом, поне́сли кару вічного огню, і поставлені в при́клад, — (aiōnios )
Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios )
8 так само буде й цим снови́дам, що опоганюють тіло, пого́рджують вла́дами, зневажають слави.
Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
9 І сам арха́нгол Михаїл, коли сперечався з дияволом і говорив про Мойсеєве тіло, не нава́жився винести суду зневажливого, а сказав: „Хай Господь доко́рить тобі!“
Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
10 А ці зневажають, чого не знають; а що знають із природи, як німа звірина́, то й у тому псуються.
Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
11 Горе їм, бо пішли вони дорогою Каїновою, і попали в обману Валаа́мової заплати, і загинули в бунті Коре́я!
Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
12 Вони скелі підводні на ваших вече́рях любови, бо з вами без стра́ху їдять та себе попаса́ють; хмари безводні, що носяться вітром; осінні дере́ва безплідні, двічі померлі, ви́корінені;
Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
13 люті хвилі мо́рські, що з піною викидають власний сором; зорі блудні́, що для них морок те́мряви береже́ться повік. (aiōn )
Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn )
14 Про них же звіщав був Ено́х, сьомий від Ада́ма, і казав: „Ось іде Госпо́дь зо Своїми десятками тисяч святих,
Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
15 щоб суд учинити над усіма́, і винуватити всіх безбожних за всі вчинки безбожности їхньої, що безбожно нако́їли, та за всі жорстокі слова, що їх говорили на Нього безбожні грішники“.
don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
16 Це ре́мствувачі, незадоволені з долі своєї, що ходять у своїх пожадливостях, а уста їхні говорять чванли́ве; вони вихваляють особи для зи́ску!
Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
17 А ви, улюблені, згадуйте слова́, що їх давніше казали апо́столи Господа нашого Ісуса Христа,
Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
18 які вам говорили: „За останнього ча́су будуть глузії́, що ходитимуть за своїми пожадливостями та безбожністю“.
Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
19 Це ті, хто відлу́чується від єдности, тілесні, що духа не мають.
Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
20 А ви, улюблені, будуйте себе найсвятішою вашою вірою, моліться у Дусі Святім,
Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
21 бережіть себе сами́х у Божій любові, і чекайте милости Господа на́шого Ісуса Христа для вічного життя. (aiōnios )
Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios )
22 І до одних, хто вагається, будьте милости́ві,
Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
23 спасайте і виривайте з огню, а до інших будьте милосердні зо стра́хом, і нена́видьте навіть одежу, опоганену від тіла!
ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
24 А Тому́, Хто може вас зберегти від упадку, і поставити перед Своєю славою непорочними в радості,
To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
25 Єдиному премудрому Богові, Спасителеві нашому через Ісуса Христа, Господа нашого, слава, могутність, сила та вла́да перше всього віку, і тепер, і на всі віки! Амі́нь. (aiōn )
Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn )