< Йов 22 >
1 І заговорив теманянин Еліфа́з та й сказав:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 „Чи для Бога люди́на кори́сна? Бо мудрий кори́сний самому собі!
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 Хіба Всемогу́тній бажає, щоб ти ніби праведним був? І що за ко́ристь Йому, як дороги свої ти вважаєш невинними сам?
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 Чи Він буде карати, тебе боячи́сь, і чи пі́де з тобою на суд?
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 Хіба твоє зло не велике? Таж твоїм беззако́нням немає кінця!
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 Таж з братів своїх брав ти заста́ву даремно, а з наго́го одежу стягав!
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 Не поїв ти водою знемо́женого, і від голодного стримував хліб.
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 А си́льна люди́на — то їй оцей край, і поче́сний у ньому сидітиме.
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 Ти напо́рожньо вдів відсилав, і сирі́тські раме́на гноби́лись, —
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 тому па́стки тебе оточи́ли, і жахає тебе наглий страх,
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 твоє світло стемні́ло, нічого не бачиш, і велика вода закриває тебе.
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 Чи ж Бог не високий, як небо? Та на зо́рі уго́ру поглянь, які стали високі вони!
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 А ти кажеш: „Що ві́дає Бог? Чи судитиме Він через млу?
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 Хмари — завіса Йому, й Він не бачить, і ходить по кру́зі небесному“.
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Чи ти будеш триматись дороги відвічної, що нею ступа́ли безбожні,
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 що невча́сно були вони згу́блені, що річка розлита, підвалина їх,
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 що до Бога казали вони: „Відступися від нас!“та: „Що́ зробить для нас Всемогутній?“
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 А Він доми їхні напо́внив добром! Але віддалилась від мене порада безбожних!
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 Справедливі це бачать та ті́шаться, і насміхається з нього невинний:
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 „Справді ви́гублений наш противник, а останок їх ви́жер огонь!“
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 Заприязни́ся із Ним, та й май спо́кій, — цим при́йде на тебе добро́.
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Зако́на візьми з Його уст, а слова Його в серце своє поклади.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 Якщо ве́рнешся до Всемогутнього, — будеш збудо́ваний, і віддали́ш беззаконня з наметів своїх.
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 І викинь до по́роху золото, і мов камінь з потоку офі́рське те золото, —
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 і буде тобі Всемогу́тній за золото та за срі́бло блискуче тобі!
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Бо тоді Всемогутнього ти покохаєш і до Бога піді́ймеш обличчя своє, —
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 будеш благати Його — й Він почує тебе, і ти обітниці свої надолу́жиш.
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 А що́ постано́виш, то ви́повниться те тобі, й на дорогах твоїх буде ся́яти світло.
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 Бо знижує Він спину пи́шного, хто ж смиренний, тому помагає.
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 Рятує Він і небезви́нного, і той чистото́ю твоїх рук урято́ваний буде“.
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”