< Ісая 9 >
1 Бо не буде темноти для того, хто ути́скуваний. Перша пора злегкова́жила була край Завуло́нів та край Нефтали́мів, а остання просла́вить дорогу примо́рську, другий бік Йорда́ну, окру́гу поганів.
Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
2 Наро́д, який в те́мряві ходить, Світло велике побачить, і над тими, хто сидить у краю тіні смерти, Світло зася́є над ними!
Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
3 Ти помно́жиш наро́д цей, Ти збільши́ш йому радість. Вони перед лицем Твоїм будуть радіти, як радіють в жнива́, як ті́шаться в час, коли ділять здо́бич!
Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
4 Бо злама́в Ти ярмо́ тягару́ його, і ки́я з раме́на його, жезло його пригноби́теля, як за днів Мадія́ма.
Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
5 Усякий бо чобіт військо́вий, що гу́пає гу́чно, та оде́жа, попля́млена кров'ю, — стане все це поже́жею, за ї́жу огню!
Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
6 Бо Дитя народи́лося нам, да́ний нам Син, і вла́да на раме́нах Його, і кликнуть ім'я́ Йому: Ди́вний Пора́дник, Бог сильний, Отець вічности, Князь миру.
Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
7 Без кінця́ буде мно́житися панува́ння та мир на троні Давида й у ца́рстві його, щоб поставити міцно його й щоб підпе́рти його правосу́ддям та правдою відтепе́р й аж навіки, — ре́вність Господа Савао́та це зробить!
Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
8 Проти Якова слово послав був Госпо́дь, а впало воно на Ізра́їля,
Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
9 і пізна́є наро́д, увесь він, Єфре́м та мешканець Самарі́ї, що говорять з пихо́ю й наду́тістю се́рця:
Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
10 „Попа́дали цегли, а ми побуду́ємо з ка́меня те́саного, сікомо́ри позру́бувано, — та замінимо їх ке́драми!“
“Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
11 Та над ним Господь зміцнив противників Реціна, а його ворогів нацькува́в:
Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
12 Арама попе́реду, а филисти́млян поза́ду, і поже́рли Ізраїля ці́лою па́щею. При цьо́му всьому не відвернувсь Його гнів, і ви́тягнена ще рука Його!
Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
13 Та наро́д не зверну́вся до Того, Хто вра́зив його, і не шукали Господа Саваота.
Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
14 Тому́ то Господь відсік від Ізраїля го́лову й хвіст, пальму й очерети́ну за одного дня.
Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
15 Стари́й та поважа́ний — це та голова, а пророк, що навчає неправди, це хвіст.
dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
16 І сталося, що повода́тарі цього наро́ду зроби́лися зві́дниками, і гинуть прова́джені ними.
Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
17 Тому́ то його юнака́ми радіти не буде Госпо́дь, а до сирі́т його й його вдів милосердя не матиме, бо кожен безбожний й злочи́нець, і зло́бне всі уста говорять. При цьому всьому не відверну́всь Його гнів, і ви́тягнена ще рука Його!
Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
18 Бо зло́ба горить, як огонь, пожира́є терни́ну й будя́ччя, і пала́є по за́пустах лісу, і кру́тяться вверх стовпи диму.
Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
19 Від лютости Господа Саваота земля загори́ться, і стане наро́д, як пожи́ва огню, і не пощади́ть жоден брата свого́!
Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
20 І різати буде право́руч, та бу́де голодний, і же́ртиме зліва, але не наси́титься, кожен же́ртиме тіло раме́на свого́:
A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
21 Манасі́я — Єфре́ма, а Єфре́м — Манасі́ю, ра́зом обоє на Юду. При цьому всьому не відверну́всь Його гнів, і ви́тягнена ще рука Його!
Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.