< Ісая 48 >
1 Послухайте це, доме Яковів, що зве́тесь іме́нням Ізраїлевим, і що вийшли із Юдиних вод, що кляне́теся Йме́нням Господнім та Бога Ізраїля згадуєте, хоч не в правді та не в справедливості!
“Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
2 Бо від міста святого вони прозива́ються та на Бога Ізраїлевого спира́ються, — Йому Йме́ння Госпо́дь Савао́т!
ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
3 Я відда́вна звіща́в про минуле, — із уст Моїх вийшло воно й розповів Я про нього, рапто́вно зробив, — і прийшло.
na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
4 Тому́, що Я знав, що впе́ртий ти є, твоя ж шия — то м'я́зи залізні, а чо́ло твоє — мідяне́,
Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
5 то звіщав Я відда́вна тобі, іще поки прийшло, розповів Я тобі, щоб ти не говорив: „Мій божо́к це зробив, а про це наказав мій бовва́н та мій і́дол“.
Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
6 Ти чув, — перегля́нь усе це; і ви хіба не визнає́те цього́? Тепер розповів Я тобі новини́ й таємни́ці, яких ти не знав.
Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
7 Тепе́р вони ство́рені, а не відда́вна, а пе́ред цим днем ти не чув був про них, щоб не сказати: „Оце я їх знав“.
Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
8 Та не чув ти й не знав, і відда́вна ти не відкривав свого ву́ха, бо Я знав, що напе́вно ти зра́диш, і зва́но тебе від утро́би: пере́вертень.
Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
9 Ради Йме́ння Свого́ Я спиня́ю Свій гнів, і ради слави Своєї Я стри́муюся проти те́бе, щоб не зни́щити тебе.
Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
10 Оце перетопи́в Я тебе, але не як те срі́бло, у го́рні недолі тебе досліди́в.
Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
11 Ради Себе, ради Себе роблю́, бо як буде збезче́щене Йме́ння Моє? А іншому слави Своєї не дам.
Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
12 Почуй Мене, Якове та Ізраїлю, Мій поклика́ний: Це Я, Я перший, також Я останній!
“Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
13 Теж рука Моя землю закла́ла, і небо напну́ла прави́ця Моя, — Я закли́чу до них — і вони стануть ра́зом.
Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
14 Зберіться ви всі та й послухайте: Хто́ серед вас розповів був про те? Кого Господь любить, вчи́нить волю Його в Вавилоні, раме́но ж Його на халде́ях.
“Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
15 Я, Я говорив і покликав його, спрова́див його, і він на дорозі своїй буде мати пово́дження.
Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
16 Набли́зьтесь до Мене, послухайте це: Споконві́ку Я не говорив потає́мно; від ча́су, як ді́ялось це, Я був там. А тепер послав Мене Господь Бог та Його Дух.
“Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
17 Гак говорить Господь, твій Відкупи́тель, Святий Ізраїлів: Я — Господь, Бог твій, що навчає тебе про кори́сне, що провадить тебе по дорозі, якою ти маєш ходити.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
18 О, коли б ти прислу́хувався до Моїх заповідей, то був би твій спо́кій, як рі́чка, а твоя справедли́вість, немов морські хвилі!
Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
19 А насі́ння твого було б, як піску́, а наща́дків твого́ живота́ — немов зе́рнят його́, і ви́тяте й ви́гублене не було б твоє йме́ння із-перед обличчя Мого́!
Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
20 Ви́рушіть із Вавилону, втечі́ть від халде́їв, радісним співом звісті́ть, оце розголосі́ть, аж до кра́ю землі рознесіть це, скажіть: Господь викупив раба Свого Якова!
Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
21 І спра́ги не знали вони на пустинях, якими прова́див Він їх: воду з скелі пустив їм, — Він скелю розбив — і вода потекла́!
Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
22 Для безбожних споко́ю немає, говорить Господь.
“Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.