< До галатів 1 >

1 Апо́стол Павло́, поставлений ні від людей, ані від чоловіка, але́ від Ісуса Христа й Бога Отця, що з мертвих Його воскресив,
Wannan Bulus manzo ne. Manzancina kuwa, bai zo daga mutane ba ko mutum, amma ta wurin Yesu Almasihu da Allah Uba wanda da ya tashe shi daga matattu.
2 і присутня зо мною вся браття, до Церко́в галаті́йських:
Ni da dukan 'yan'uwa da nake tare da su a nan, ina rubuto maku ku iklisiyoyi da ke a Galatiya.
3 благодать вам і мир від Бога, Отця нашого, і Господа Ісуса Христа,
Alheri zuwa gare ku da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangjinmu Yesu Almasihu,
4 що за наші гріхи дав Само́го Себе, щоб від злого сучасного віку нас визволити, за волею Бога й Отця нашого, — (aiōn g165)
wanda ya ba da kansa domin zunubanmu saboda ya kubutar da mu daga wannan mugun zamani, bisa ga nufin Allah da Ubanmu. (aiōn g165)
5 Йому слава на віки́ вічні, амі́нь! (aiōn g165)
Daukaka ta tabbata a gare shi har abada abadin. (aiōn g165)
6 Дивуюся я, що ви так скоро відхи́люєтесь від того, хто покликав Христовою благодаттю вас, на іншу Єва́нгелю,
Na yi mamaki kwarai yadda kuka juya da sauri zuwa wata bishara daban. Na yi mamakin cewa kuna juyawa daga shi wanda ya kira ku ta wurin alherin Almasihu.
7 що не інша вона, але деякі є, що вас непокоять, і хочуть перевернути Христову Єва́нгелію.
Ba wata bishara, amma akwai wadansu mutane da suke kawo maku rudani kuma suna so su gurbata bisharar Almasihu.
8 Але якби й ми або а́нгол із неба зачав благовісти́ти вам не те, що ми вам благовісти́ли, — нехай буде прокля́тий!
Amma, ko da mu ne ko mala'ika daga sama ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda muka yi shelar ta, la'ananne ne.
9 Як ми перше казали, і тепер знов кажу́: коли хто вам не те благовісти́ть, що ви прийняли́, — нехай буде прокля́тий!
Kamar yadda muka fadi maku a da, yanzu kuma ina sake fada, “Idan wani ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda kuka karba, la'ananne ne.”
10 Бо тепер чи я в людей шукаю призна́ння чи в Бога? Чи лю́дям дба́ю я догоджа́ти? Бо коли б догоджав я ще лю́дям, я не був би рабо́м Христовим.
To yanzu ina neman shaidar mutane ne ko Allah? Ina neman in gamshi mutane ne? Idan har yanzu ina kokarin in gamshi mutane ne, ni ba bawan Almasihu ba ne.
11 Звіщаю ж вам, браття, що Єва́нгелія, яку я благовісти́в, — вона не від людей.
Ina son ku sani fa 'yan'uwa, cewa bisharar da nake shelar ta ba daga mutane take ba.
12 Бо я не прийняв, ні навчився її від люди́ни, але об'явленням Ісуса Христа.
Ban karbe ta daga mutum ba, ba ma wanda ya koyar mani A maimakon haka, ta wurin wahayin Yesu Almasihu ne zuwa gare ni.
13 Чули бо ви про моє поступо́вання перше в юдействі, що Божу Церкву жорсто́ко я переслідував та руйнував її.
Kun riga kun ji game da rayuwa ta a da cikin Yahudanci, yadda da nake da kwazon tsananta wa iklisiyar Allah fiye da misali kuma ina lalatar da ita.
14 І я перевищував в юдействі багатьох своїх рове́сників роду мого, бувши запе́клим прихильником моїх отці́вських переда́нь.
Ina gaba-gaba cikin Yahudanci fiye da yawancin tsararrakina. A kwazo kuwa fiye da kima game da al'adun ubannina.
15 Коли ж Бог, що вибрав мене від утро́би матері моєї і покликав благода́ттю Своєю, уподобав
Amma ya gamshi Allah ya zabe ni daga cikin mahaifiyata. Ya kira ni ta wurin alherinsa.
16 виявити мною Сина Свого, щоб благовістив я Його між поганами, — я не радився зараз із тілом та кров'ю,
Ya bayyana dansa a gareni, saboda in yi shelar sa cikin al'ummai. Nan da nan, ban nemi shawarar nama da jini ba
17 і не відправився в Єрусалим до апо́столів, що передо мною були, а пішов я в Ара́бію, і зно́ву вернувся в Дама́ск.
kuma ban tafi Urushalima ba wurin wadanda suka zama manzanni kafin ni. Maimakon haka sai na tafi Arebiya, daga nan sai na dawo Dimashku.
18 По трьох ро́ках пото́му пішов я в Єрусалим побачити Ки́фу, і в нього пробув днів із п'ятнадцять.
Bayan shekara uku na je Urushalima don in san Kefas, na zauna da shi na kwana goma sha biyar.
19 А іншого з апо́столів я не бачив, крім Якова, брата Господнього.
Amma ban ga ko daya daga cikin manzannin ba sai Yakubu kadai, dan'uwan Ubangiji.
20 А що вам пишу́, ось кажу́ перед Богом, що я не обманюю!
Duba, a gaban Allah, ba karya nake yi ba cikin abin da na rubuta maku.
21 Пото́му пішов я до си́рських та кілікі́йських країн.
Daga nan sai na je lardin Suriya da Kilikiya.
22 Церква́м же Христовим в Юдеї я знаний не був особисто, -
Har a lokacin babu wanda ya san ni a fuska a iklisiyoyin Yahudiya da suke cikin Almasihu,
23 тільки чули вони, що той, що колись переслідував їх, благовісти́ть тепер віру, що колись руйнував був її.
amma sai labari kawai suke ji, “Wanda a da yake tsananta mana yanzu yana shelar bangaskiyar da a da yake rusarwa.”
24 І сла́вили Бога вони через мене!
Suna ta daukaka Allah saboda ni.

< До галатів 1 >