< Дії 6 >

1 Тими ж днями, як учнів намно́жилось, зачали́ нарікати на євреїв огре́чені, що в щоденному служі́нні їхні вдовиці зане́дбані.
A waɗannan kwanaki, sa’ad da yawan almajirai suke ƙaruwa, sai Yahudawan masu jin Hellenanci a cikinsu suka yi gunaguni a kan Yahudawan da suke Ibraniyawa domin ba a kula da gwaurayensu a wajen raba abinci na yau da kullum.
2 Тоді ті Дванадцять покликали багатьо́х учнів та й сказали: „Нам не ли́чить покинути Боже Слово, і служити при стола́х.
Saboda haka Sha Biyun nan suka tara dukan almajirai wuri ɗaya, suka ce, “Bai zai yi kyau mu bar hidimar maganar Allah don mu shiga hidimar abinci ba.
3 Отож, браття, ви́глядіть із-поміж себе сімох мужів доброї слави, повних Духа Святого та мудрости, — їх поставимо на службу оцю.
’Yan’uwa, ku zaɓi mutum bakwai daga cikinku waɗanda aka sani suna cike da Ruhu da kuma hikima. Mu kuwa za mu danƙa musu wannan aiki
4 А ми перебува́тимемо за́вжди в молитві та в служі́нні слову“.
mu kuwa mu mai da halinmu ga yin addu’a da kuma hidimar maganar Allah.”
5 І всім лю́дям сподо́балося оце слово, і обрали Степа́на, мужа повного віри та Духа Святого, і Пилипа, і Про́хора та Никано́ра, і Ти́мона та Парме́на, і нововірця Миколу з Антіохії, —
Wannan shawarar kuwa ta gamshi dukan ƙungiyar. Sai suka zaɓi Istifanus, mutumin da yake cike da bangaskiya da kuma Ruhu Mai Tsarki; da Filibus, Burokorus, Nikano, Timon, Farmenas, da Nikolas daga Antiyok, wanda ya tuba zuwa Yahudanci.
6 їх поставили перед апо́столів, і, помолившись, вони руки поклали на них.
Suka gabatar da waɗannan mutane wa manzanni, waɗanda kuwa suka yi addu’a, suka ɗibiya hannuwansu a kansu.
7 І росло Слово Боже, і ду́же мно́жилося число учнів у Єрусалимі, і дуже багато священиків були слухня́ні вірі.
Saboda haka maganar Allah ta yaɗu. Yawan almajirai a Urushalima kuwa ya yi saurin ƙaruwa, firistoci masu yawa kuma suka zama masu biyayya ga wannan bangaskiya.
8 А Степан, повний віри та сили, чинив між наро́дом великі знаме́на та чуда.
To, Istifanus, mutum cike da alheri da ikon Allah, ya aikata manyan ayyukan da alamu masu banmamaki a cikin mutane.
9 Тому дехто повстав із синагоги, що зветься ліберти́нська, і кірінейська, і олександрійська, та з тих, хто походить із Кілікі́ї та з Азії, і зачали́ сперечатись із Степа́ном.
Sai hamayya ta taso daga’yan ƙungiyar Majami’a na’Yantattu (kamar yadda ake kiransu), Yahudawan Sairin da Alekzandariya da kuma lardunan Silisiya da Asiya. Mutanen nan suka fara muhawwara da Istifanus,
10 Але всто́яти вони не могли проти мудрости й Духа, що він Ним говорив.
amma ba su iya cin nasara kan hikimarsa ko kuma a kan Ruhu wanda ta wurinsa ne ya magana ba.
11 Тоді вони підмовили людей, що казали, ніби чули, як він богозневажні слова́ говорив на Мойсея та Бога.
Sa’an nan a asirce suka zuga waɗansu mutane su ce, “Mun ji Istifanus ya faɗa kalmomin saɓo game da Musa da kuma Allah.”
12 І людей попідбу́рювали, і старших та книжників, і, напавши, схопи́ли його, і припрова́дили в синедріо́н.
Ta haka suka tā da hankalin mutane da dattawa da kuma malaman dokoki. Suka kama Istifanus suka kawo shi a gaban Majalisa.
13 Також свідків фальшивих поставили, які говорили: „Чоловік оцей богознева́жні слова́ безпере́стань говорить на це святе місце та проти Зако́ну.
Suka kawo masu ba da shaidar ƙarya, waɗanda suka ba da shaida cewa, “Wannan mutum ba ya rabuwa da maganar banza a kan wurin nan mai tsarki da kuma doka.
14 Бо ми чули, як він говорив, що Ісус Назаряни́н зруйнує це місце та змінить звича́ї, які передав нам Мойсей“.
Gama mun ji shi yana cewa wannan Yesu Banazare zai rushe wurin nan ya kuma canja al’adun da Musa ya ba mu.”
15 Коли всі, хто в синедріоні сидів, на нього споглянули, то бачили лице його, — як лице Ангола!
Dukan waɗanda suke zaune a Majalisar suka kafa wa Istifanus ido, suka kuma ga fuskarsa ta yi kama da ta mala’ika.

< Дії 6 >