< Дії 26 >
1 А Агріппа сказав до Павла: „Дозволяємо тобі говорити про себе само́го“. Павло тоді простягнув руку, і промовив у своїй обороні:
Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “An ba ka izini ka yi magana.” Saboda haka Bulus ya yi alama da hannunsa ya fara kāriyarsa.
2 „О ца́рю Агріппо! Уважаю себе за щасливого, що сьогодні я перед тобою боронитися маю з усьо́го, у чім мене винуватять юдеї,
Ya ce, “Sarki Agiriffa, na yi sa’a da na tsaya a gabanka yau yayinda nake kāriyata game da dukan zargin Yahudawa,
3 особливо ж тому́, що ти знаєш усі юдейські звича́ї та супере́чки. Тому я прошу́ мене вислухати терпля́че.
musamman ma domin ka saba sosai da dukan al’adun Yahudawa da kuma maganganunsu. Saboda haka ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
4 А життя моє зма́лку, що споча́тку точилося в Єрусалимі серед наро́ду мого, знають усі юдеї,
“Yahudawa duk sun san yadda na yi rayuwa tun ina yaro, daga farkon rayuwata a ƙasarmu da kuma a Urushalima.
5 які відають зда́вна мене, аби тільки схотіли засві́дчити, — що я жив фарисеєм за найдокладнішою сектою нашої віри.
Sun san ni tun da daɗewa za su kuwa shaida, in suna so, cewa bisa ga ɗarikar addininmu mafi tsanani, na yi rayuwar Bafarisiye ne.
6 І тепер я стою отут су́джений за надію обі́тниці, що Бог дав ії нашим отцям,
Yanzu kuwa saboda begena cikin abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari ne, ake mini shari’a yau.
7 а її викона́ння чекають побачити наші дванадцять племен, слу́жачи Богові безперестанно вдень та вночі. За цю надію, о ца́рю, мене винуватять юдеї!
Wannan shi ne alkawarin da kabilanmu goma sha biyu suke bege su ga cikawarsa, yayinda suke bauta wa Allah da himma dare da rana. Ya Sarki, saboda wannan bege ne fa Yahudawa suke zargena.
8 Чому ви вважаєте за неймовірне, що Бог воскрешає померлих?
Don me wani a cikinku zai yi shakka cewa Allah yana tā da matattu?
9 Правда, ду́мав був я, що мені нале́жить чинити багато ворожого проти Ймення Ісуса Назаряни́на,
“Ni ma a dā na tabbata cewa ya kamata in yi duk abin da zan iya yi domin in yi gāba da sunan Yesu Banazare.
10 що я в Єрусалимі й робив, і багато кого зо святих до в'язниць я замкнув, як отримав був вла́ду від первосвящеників; а як їх убивали, я голос давав проти них.
Abin da na yi ke nan a Urushalima. Da izinin manyan firistoci na sa tsarkaka da yawa a kurkuku, sa’ad da kuma ake kashe su, nakan ka da ƙuri’ata gāba da su.
11 І часто по всіх синагогах караючи їх, до богозневаги примушував я, а лютуючи ве́льми на них, переслідував їх навіть по закордонних містах.
Sau da dama nakan bi majami’a-majami’a, in sa a yi musu hukunci. Na kuma yi ƙoƙarin tilasta su su yi saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.
12 Коли в цих справах я йшов до Дамаску зо вла́дою та припору́ченням первосвящеників,
“A cikin irin tafiye-tafiyen nan ne ina kan hanya zuwa Damaskus tare da izini daga manyan firistoci.
13 то опі́вдні, о ца́рю, на дорозі побачив я світло із неба, ясніше від світлости сонця, що ося́яло мене та тих, хто разом зо мною йшов!
Da tsakar rana, ya sarki, sa’ad da nake kan hanya, sai na ga wani haske daga sama, fiye da hasken rana, yana haskakawa kewaye da ni da abokan tafiyata.
14 І як ми всі повалились на землю, я голос почув, що мені говорив єврейською мовою: „Савле, Савле, — чому ти Мене переслідуєш? Трудно тобі бити ногою колю́чку!“
Dukanmu muka fāɗi ƙasa, na kuwa ji wata murya tana ce mini da harshen Arameyik, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Yana da wuya ka shuri tsinken tsokanar dabba.’
15 А я запитав: „Хто Ти, Господи?“А Він відказав: „Я Ісус, що Його переслідуєш ти.
“Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
16 Але підведи́ся, і стань на ноги свої. Бо на те Я з'явився тобі, щоб тебе вчинити слугою та свідком того, що ти бачив та що Я відкрию тобі.
Yanzu ka tashi, ka tsaya da ƙafafunka. Na bayyana a gare ka don in naɗa ka bawa da kuma mai shaidar abin da ka gani game da ni da kuma abin da zan nuna maka.
17 Визволяю тебе від твого наро́ду та від поган, до яких Я тебе посилаю, —
Zan tsirar da kai daga mutanenka da kuma daga Al’ummai. Ina aikan ka zuwa gare su domin
18 відкрити їм очі, щоб вони наверну́лись від те́мряви в світло та від сатани́ної вла́ди до Бога, щоб вірою в Мене отримати їм дарува́ння гріхів і насліддя з освяченими“.
ka buɗe idanunsu su kuwa juyo daga duhu zuwa haske, daga mulkin Shaiɗan kuma zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai da kuma matsayi a cikin waɗanda aka tsarkake ta wurin bangaskiya a cikina.’
19 Через це я, о ца́рю Агріппо, не був супротивний видінню небесному,
“Saboda haka fa, Sarki Agiriffa, ban yi rashin biyayya ga wahayin nan daga sama ba.
20 але ме́шканцям перше Дамаску, потім Єрусалиму й усякого кра́ю юдейського та поганам я проповідував, щоб пока́ялися й наверну́лись до Бога, і чинили діла, гі́дні покая́ння.
Da farko ga waɗanda suke a Damaskus, sa’an nan ga waɗanda suke a Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya, da kuma ga Al’ummai su ma, na yi wa’azi don su tuba su juyo ga Allah su kuma tabbatar da tubansu ta wurin ayyukansu.
21 Через це юдеї в святині схопи́ли мене та й хотіли роздерти.
Shi ya sa Yahudawa suka kama ni a filin haikali suka kuma yi ƙoƙarin kashe ni.
22 Але, поміч від Бога одержавши, я стою́ аж до дня сьогоднішнього та свідкую мало́му й великому, нічого не розповідаючи, окрім того, що сказали Пророки й Мойсей, що статися має, —
Amma na sami taimakon Allah har yă zuwa yau. Yanzu ga ni a tsaye a nan, ina shaida ga babba da yaro. Ba na faɗin kome fiye da abin da annabawa da Musa suka ce zai faru,
23 що має Христос постраждати, що Він, як перший воскреснувши з мертвих, проповідувати буде світло народові й поганам!“
cewa Kiristi zai sha wahala, kuma a matsayin wanda yake na fari da zai tashi daga matattu, zai yi shelar haske ga mutanensa da kuma Al’ummai.”
24 Коли ж він боронився отак, то Фест проказав гучни́м голосом: „Дурієш ти, Павле! Велика наука доводить тебе до нерозуму“!
A nan ne fa Festus ya tsai da kāriyar Bulus. Ya yi ihu ya ce, “Bulus! Kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”
25 А Павло: „Не дурію — сказав, — о Фесте достойний, але провіщаю слова правди та щирого розуму.
Bulus ya amsa ya ce, “Ba na hauka, ya mafifici Festus. Abin da nake faɗi gaskiya ne da kuma mai kyau.
26 Цар бо знає про це, — до нього з відвагою я й промовляю. Бо не гада́ю я, щоб із цього щобудь схова́лось від нього, — бо не в за́кутку ді́ялось це.
Sarki ya san waɗannan abubuwa, ina kuma iya yin magana da shi a sake. Na tabbata cewa ba ɗaya daga cikin waɗannan da ya kuɓuce saninsa, domin ba a ɓoye aka yi shi ba.
27 Чи віруєш, ца́рю Агріппо, Пророкам? Я знаю, що віруєш“.
Sarki Agiriffa ka gaskata da annabawa? Na san ka gaskata.”
28 Агріппа ж Павлові: „Ти малощо не намовляєш мене, щоб я став християни́ном“.
Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “Kana tsammani cewa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kana so ka mai da ni Kirista?”
29 А Павло: „Благав би я Бога, щоб чи мало, чи багато, — не тільки но ти, але й усі, хто чує сьогодні мене, зробились такими, як і я, крім оцих ланцюгів“.
Bulus ya amsa ya ce, “Ko a ɗan lokaci, ko a lokaci mai yawa, ina addu’a ga Allah cewa, ba kai kaɗai ba amma duk waɗanda suke saurare ni a yau su zama abin da nake, sai dai ban da sarƙoƙin nan.”
30 І встав цар та намісник, і Верні́ка та ті, хто з ними сидів.
Sai sarki ya tashi, haka kuma gwamna da Bernis da kuma waɗanda suke zaune tare da su.
31 І на́бік вони відійшли, і розмовляли один до одно́го й казали: „Нічого, ва́ртого смерти або ланцюгів, чоловік цей не робить!“
Suka bar ɗakin, kuma yayinda suke magana da juna, sai suka ce, “Wannan mutum ba ya yin kome da ya isa kisa ko dauri.”
32 Агріппа ж до Феста сказав: „Міг би бути відпу́щений цей чоловік, якби не відкликавсь був до ке́саря“
Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Da ba don wannan mutum ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba da an sake shi.”