< 2 Тимофію 2 >
1 Отож, сину мій, зміцняйся в благода́ті, що в Христі Ісусі вона!
Kai kuma, ɗana, ka yi ƙarfi cikin alherin da yake cikin Kiristi Yesu.
2 А що чув ти від мене при багатьо́х свідках, те передай вірним лю́дям, що будуть спроможні й інших навчити.
Abubuwan da ka ji na faɗa a gaban shaidu masu yawa kuwa ka danƙa wa amintattun mutane waɗanda su ma za su iya koya wa waɗansu.
3 А ти терпи лихо, як добрий воя́к Христа Ісуса!
Ka jure wa shan wahala tare da mu kamar soja mai kyau na Kiristi Yesu.
4 Бо жоден воя́к не в'яжеться в справи життя, аби догодити тому, хто ві́йсько збирає.
Ba wanda yake aikin soja da zai sa kansa a sha’anin mutumin da ba ya aikin soja, domin yakan so yă gamshi wanda ya ɗauke shi soja.
5 А як хто йде на зма́ги, то вінка́ не одержує, якщо незако́нно змага́ється.
Haka ma, in wani ya yi gasa a matsayi shi ɗan wasa ne, ba ya sami rawanin nasara, sai in ya yi gasar bisa ga dokoki.
6 Трудящому хліборо́бові нале́житься першому покуштувати з плоду.
Manomi mai aiki sosai ya kamata yă zama na fari wajen samun rabon amfanin gona.
7 Розумій, що́ я говорю́. А Госпо́дь нехай дасть тобі розум у всьому.
Ka yi tunani a kan abin da nake faɗi, gama Ubangiji zai ba ka ganewa cikin dukan wannan.
8 Пам'ятай про Ісуса Христа з насіння Дави́дового, що воскрес із мертвих, за моєю Єва́нгелією,
Ka tuna da Yesu Kiristi, wanda aka tā da shi daga matattu, zuriyar Dawuda, wanda shi ne bisharata,
9 за яку я терплю́ муки аж до ув'я́знення, як той злочи́нець. Але Сло́ва Божого не ув'язни́ти!
wadda nake shan wahala har ga daurin sarƙa kamar mai laifi. Amma Maganar Allah ba a daure take ba.
10 Через це перено́шу я все ради ви́браних, щоб і вони доступили спасі́ння, що в Христі Ісусі, зо славою вічною. (aiōnios )
Saboda haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton da yake cikin Kiristi Yesu, tare da madawwamiyar ɗaukaka. (aiōnios )
11 Вірне слово: коли ра́зом із Ним ми померли, то й жи́тимемо ра́зом із Ним!
Ga wata magana tabbatacciya, “In muka mutu tare da shi, za mu rayu tare da shi;
12 А коли терпимо́, то будемо ра́зом тако́ж царюва́ти. А коли відцураємось, то й Він відцурається нас!
in muka jimre, za mu yi mulki tare da shi. In muka yi mūsunsa, shi ma zai yi mūsunmu;
13 А коли ми невірні, зостається Він вірним, бо не може зректися Само́го Себе!
in ba mu da aminci, shi dai mai aminci ne, domin shi ba zai iya mūsun kansa ba.”
14 Нагадуй про це й заклинай перед Богом, щоб не спереча́лись словами, бо ніна́що воно, хіба слухача́м на руїну.
Ka riƙa tuna masu da haka, ka kuma gama su da Allah, kada su yi jayayya a kan maganganu, don ba ta da wani amfani, sai ɓad da masu ji kawai take yi.
15 Силку́йся поставити себе перед Богом гідним, працівнико́м бездоганним, що вірно навчає науки правди.
Ka yi iyakacin ƙoƙarinka ka gabatar da kanka a gaban Allah a matsayin wanda aka amince da shi, ma’aikaci wanda ba shi da dalilin jin kunya wanda kuma yake fassara kalmar gaskiya daidai.
16 Стережися ж базі́кань марни́х, бо вони ще більше провадять до безбожности,
Ka yi nesa da maganganun banza na rashin tsoron Allah, gama waɗanda suka mai da hankali ga yin waɗannan za su ƙara zama marasa tsoron Allah.
17 а їхнє слово, як рак, буде ши́ритися. Від таких Гімене́й і Філі́т,
Koyarwarsu za tă bazu kamar ruɓaɓɓen gyambo. A cikinsu akwai Himenayus da Filetus,
18 що вони погрішилися в правді, казавши, що воскресі́ння було вже, і віру деяких руйнують.
waɗanda suka bauɗe daga gaskiya. Suna cewa tashin matattu ya riga ya faru, suna kuma ɓata bangaskiyar waɗansu.
19 Та однако стоїть міцна́ Божа основа та має печатку оцю: „Господь знає тих, хто Його“, та: „Нехай від неправди відсту́питься всякий, хто Господнє Ім'я́ називає!“
Duk da haka, ƙaƙƙarfan tushen nan na Allah yana nan daram, an hatimce shi da wannan rubutu, “Ubangiji ya san waɗanda suke nasa,” da kuma, “Duk wanda ya bayyana yarda ga sunan Ubangiji, to, dole yă yi nesa da aikata mugunta.”
20 А в великому домі знахо́диться по́суд не тільки золотий та срібний, але й дерев'яний та гли́няний, і одні посу́дини на честь, а другі на не́честь.
A babban gida akwai kayayyakin da ba na zinariya da na azurfa kaɗai ba, amma har da na katako da na yumɓu ma; waɗansu domin hidima mai daraja waɗansu kuwa domin hidima marar daraja.
21 Отож, хто від цього очистить себе, буде по́суд на честь, освя́чений, потрібний Володареві, приготова́ний на всяке добре ді́ло.
In mutum ya tsabtacce kansa daga na farkon zai zama kayan aikin hidima mai daraja, mai amfani ga Maigida, kuma shiryayye domin yin kowane aiki mai kyau.
22 Стережися молодечих пожадли́востей, трима́йся праведности, віри, любови, миру з тими, хто Господа кличе від чистого серця.
Ka yi nesa da mugayen sha’awace-sha’awace na ƙuruciya, ka kuma bi adalci, bangaskiya, ƙauna da kuma salama, tare da waɗanda suke kira ga Ubangiji daga zuciya mai tsabta.
23 А від нерозумних та від невче́них змага́нь ухиляйся, знавши, що вони родять сварки́.
Kada wani abu yă haɗa ka da gardandamin banza da wofi, domin ka san yadda suke jawo faɗa.
24 А раб Господній не повинен свари́тись, але бути привітним до всіх, навча́льним, до ли́ха терпля́чим,
Bai kamata bawan Ubangiji yă zama mai neman faɗa ba; a maimako, dole yă nuna alheri ga kowa, mai iya koyarwa, mai haƙuri kuma.
25 що навчав би противників із ла́гідністю, чи Бог їм не дасть покая́ння, щоб правду пізнати,
Waɗanda suke gāba da shi kuwa dole yă yi musu gargaɗi cikin hankali, da fata Allah zai sa su tuba su kai ga sanin gaskiya,
26 щоб визволитися від сітки диявола, що він уловив їх для ро́блення волі своєї.
su kuma dawo cikin hankulansu su kuɓuta daga tarkon Iblis, wanda ya sa suka zama kamammu don su aikata nufinsa.