< 1 хроніки 13 >
1 І ра́дився Давид із тисячниками та з сотниками, зо всіма́ значни́ми.
Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
2 І сказав Давид до всієї Ізраїлевої грома́ди: „Якщо вам це добре, а від Господа, Бога нашого вподо́бане, пошлі́мо до наших братів, позосталих по всіх Ізраїлевих края́х, а з ними до священиків та Левитів, по містах та по їхніх пасовиськах, і нехай зберу́ться до нас.
Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
3 І вернімо ковчега нашого Бога до нас, бо не зверта́лися ми до нього за Саулових днів“.
Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
4 І сказала вся громада, щоб зробити так, бо слу́шна була та річ в оча́х усього народу.
Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
5 І зібрав Давид усього Ізраїля від єгипетського Шіхору й аж туди, де йде́ться до Хамату, щоб спрова́дити Божого ковчега з Кір'ят-Єаріму.
Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
6 І пішов Давид та ввесь Ізра́їль у Баалу, в Юдин Кір'ят-Єарім, щоб ви́нести звідти ковчега Бога, Господа, що сидить на херувимах, що ім'я́ Його приклика́ється.
Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
7 І пове́зли Божого ковчега на ново́му возі з Авінадавового дому, а Узза та Ахйо прова́дили того воза.
Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
8 А Давид та ввесь Ізраїль грали перед Божим лицем з усієї сили, — із пісня́ми, і на ци́трах, і на а́рфах, і на бу́бнах, і на цимба́лах, і на су́рмах.
Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
9 І прийшли вони аж до Кідонового то́ку, і простяг Узза свою руку, щоб підхопи́ти ковчега, бо воли нахили́ли його.
Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
10 І запалився на Уззу гнів Господній, і Він убив його за те, що простяг руку свою до ковчега. І помер він там перед Господнім лицем...
Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
11 І зажури́вся Давид тим, що Господь убив Уззу, і він назвав ім'я тому місцю: Перец-Узза, і так воно зветься аж до цього дня.
Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
12 І того дня Давид злякався Бога, говорячи: „Як я внесу́ до се́бе Божого ковчега?“
Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
13 І не повіз Давид ковчега до се́бе, до Давидового Міста, а напра́вив його до дому гатянина Овед-Едома.
Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
14 І пробува́в Божий ковчег із домом Овед-Едома в його домі три місяці. А Господь поблагослови́в дім Овед-Едома, та все, що було його́.
Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.