< До римлян 10 >

1 Браттє, бажаннє мого сердя і молитва (йде) до Бога за Ізраїля про спасеннє.
’Yan’uwa, abin da zuciyata take so da kuma addu’ata ga Allah saboda Isra’ilawa shi ne su sami ceto.
2 Сьвідкую бо їм, що ревність Божу мають, та не по розуму.
Gama na shaida su a kan suna da kishi bin Allah, sai dai kishinsu ba a bisa sani ba.
3 Не розуміючи бо праведності Божої, і шукаючи свою праведність поставити, праведності Божій не корили ся.
Da yake ba su san adalcin da yake fitowa daga Allah ba suka kuma nemi su kafa nasu, sai suka ƙi miƙa kai ga adalcin Allah.
4 Кінець бо закону - Христос, на праведність кожному віруючому.
Kiristi shi ne ƙarshen doka domin a sami adalci wa kowane mai bangaskiya.
5 Мойеей пише про праведність, що від закону; що которий чоловік робити ме се, жити ме ним.
Musa ya bayyana adalcin da yake ga Doka cewa, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
6 А та, що од віри, праведність, так говорить: Не кажи в серці твоїм: Хто зійде на небо? (се єсть: Христа звести додолу; )
Amma adalcin da yake ga bangaskiya yana cewa, “Kada ka faɗa a zuciyarka, ‘Wa zai hau sama?’” (wato, don yă sauko da Kiristi),
7 або: Хто зійде в безодню? (се єсть: Христа з мертвих угору звести.) (Abyssos g12)
“ko kuwa ‘Wa zai gangara can zurfin ƙasa?’” (wato, don yă hauro da Kiristi daga matattu). (Abyssos g12)
8 А що ж глаголе (писаннє)? Близько тебе слово в устах твоїх і в серцї твоїм, се єсть слово віри, що ми проповідуємо;
Amma mene ne aka ce? “Maganar tana kusa da kai; tana cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka,” wato, maganar bangaskiyan nan da muke shela.
9 щоб, коли визнавати меш устами твоїми Господа Ісуса, і вірувати меш в серцї твоїм, що Бог Його підняв з мертвих, ти спас ся.
Cewa in ka furta da bakinka, “Yesu Ubangiji ne,” ka kuma gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tā da shi daga matattu, za ka sami ceto.
10 Серцем бо віруєть ся на праведність, устами ж визнаєть ся на спасеннє.
Gama da zuciyarka ce kakan gaskata a kuma kuɓutar da kai, da bakinka ne kuma kake furta a kuma cece ka.
11 Глаголе бо писаннє: Всяк, хто вірує в Него, не осоромить ся.
Kamar yadda Nassi ya ce, “Duk wanda ya gaskata da shi ba zai taɓa shan kunya ba.”
12 Бо нема ріжницї між Жидовином і Греком; Він бо Господь усіх, богатий для всїх, хто призиває Його.
Gama ba bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, Ubangijin nan ɗaya shi ne Ubangijin kowa yana kuma ba da albarka a yalwace ga duk masu kira gare shi,
13 Всяк бо, хто призове імя Господнє, спасеть ся.
gama, “Duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.”
14 Як же призивати муть Того, в кого не увірували? як же вірувати муть, про кого не чули, як же чути муть без проповідаючого?
To, ta yaya za su kira ga wanda ba su gaskata ba? Ta yaya kuma za su gaskata wanda ba su taɓa ji ba? Ta yaya kuma za su ji ba tare da wani ya yi musu wa’azi ba?
15 А як же проповідати муть коли не будуть послані? яко ж писано: Що за красні ноги благовіствуючих впокій, благовіствуючих про добре?
Kuma ta yaya za su yi wa’azi in ba an aike su ba? Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Isowar masu kawo labari mai daɗi abu mai kyau ne ƙwarai!”
16 Та не всї послухали благовістя. Ісаїя бо глаголе: Господи, хто увірував голосу нашому?
Amma ba dukan Isra’ilawa ne suka karɓi labari mai daɗin nan ba. Gama Ishaya ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu?”
17 Тим же то віра (приходить) через слуханнє, слуханнє ж через слово Боже.
Saboda haka, bangaskiya takan zo ne ta wurin jin saƙo, akan ji saƙon kuma ta wurin maganar Kiristi.
18 Тільки ж глаголю: Хиба вони не чули? Нї, по всїй землі бо розійшов ся гомін їх і до кінцїв вселенної глаголи їх.
Amma ina tambaya, “Ba su ji ba ne? Tabbatacce sun ji. “Muryarsu ta tafi ko’ina a cikin duniya, kalmominsu kuma har iyakar duniya.”
19 І ще питаю: Хиба не розумів Ізраїль? Первий Мойсей глаголе: Завдам вам зависти через (тих, що) не (єсть мій) нарід, народом безумним завдам жалю вам.
Har wa yau, ina da tambaya. Shin, Isra’ila ba su fahimta ba ne? Da farko, Musa ya ce, “Zan sa ku yi kishin waɗanda ba al’umma ba; zan sa ku yi fushin al’ummar da ba ta da fahimta.”
20 Ісаїя ж зосьміливсь і глаголе: Знайшли мене ті, що не шукали, обявивсь я тим, що не питали про мене.
Ishaya kuma ya fito gabagadi ya ce, “Waɗanda ba su neme ni ba, su suka same ni; Na bayyana kaina ga waɗanda ba su ma taɓa neman sanina ba.”
21 До Їзраїля ж глаголе: Увесь день простягав я руки мої до людей непокірних і суперетних.
Amma game da Isra’ila ya ce, “Dukan yini na miƙa hannuwana ga mutane marasa biyayya da masu taurinkai.”

< До римлян 10 >