< Об'явлення 8 >
1 І коли створив сему печать, стало мовчаннє на небі, близько пів години.
Sa’ad da ya buɗe hatimi na bakwai, sai aka yi shiru a sama na kusan rabin sa’a.
2 І я бачив сім ангелів, що стояли перед Богом, і дано їм сім труб.
Sai na ga mala’iku bakwai da suke tsayawa a gaban Allah, a gare su kuwa aka ba da ƙahoni bakwai.
3 І приступив инший ангел, і став перед жертівнею, маючи золоту кадильницю; і дано йому багато пахощів, щоб положив з молитвами усїх сьвятих на жертівню золоту, що перед престолом.
Wani mala’ika, da yake da kaskon zinariyar da ake zuba turare, ya zo ya tsaya kusa da bagaden. Aka ba shi turare da yawa don yă miƙa tare da addu’o’in dukan tsarkaka a bisa bagaden zinariya a gaban kursiyin.
4 І зняв ся дим пахощів з молитвами сьвятих, від руки ангела, перед Богом,
Hayaƙin turaren tare da addu’o’in tsarkaka, suka hau zuwa gaban Allah daga hannun mala’ikan.
5 і взяв ангел кадильницю, і наповнив її огнем із жертівнї, і кинув на землю; і постали голоси, і громи, і блискавки і трясеннє.
Sai mala’ikan ya ɗauki kaskon, ya cika shi da wuta daga bagaden, ya kuma wurga shi bisan duniya; sai aka yi ta yin tsawa, ƙararraki, walƙiya, da kuma girgizar ƙasa.
6 І сїм ангелів, що мали сїм труб, готовились, щоб трубити.
Sai mala’iku bakwai ɗin nan da suke da ƙahoni bakwai suka shirya don su busa su.
7 І первий ангел затрубив, і постав град і вогонь, змішані з кровю; і спало на землю. І третя часть деревини згоріла, і вся трава зелена згоріла.
Mala’ika na fari ya busa ƙahonsa, sai ga ƙanƙara da wuta haɗe da jini, aka kuma wurga su bisan duniya. Kashi ɗaya bisa uku na duniya ya ƙone, kashi ɗaya bisa uku na itatuwa suka ƙone, dukan ɗanyar ciyawa kuma ta ƙone.
8 І другий ангел затрубив, і наче велику гору, огнем розпалену, кинуло в море. І третя часть моря стала кровю.
Mala’ika na biyu ya busa ƙahonsa, sai ga wani abu kamar babban dutse mai cin wuta, aka jefa cikin teku. Kashi ɗaya bisa uku na teku ya zama jini,
9 І погибла третя часть створіння в морю, що мала життє, і третя часть човнів знищена.
kashi ɗaya bisa uku na halittu masu rai da suke cikin tekun suka mutu, kashi ɗaya bisa uku kuma na jiragen ruwa kuma suka hallaka.
10 І третїй ангел затрубив, і впала з неба велика звізда палаюча, як смолоскип, а впала на третю часть рік і на жерела вод.
Mala’ika na uku ya busa ƙahonsa, sai wani babban tauraro mai cin wuta kamar toci, ya fāɗi daga sararin sama, a kan kashi ɗaya bisa uku na koguna da kuma a bisa maɓulɓulan ruwa
11 А ймя звїзди Полин, і стала третя часть вод наче полин, і многі люде померли од води, бо гірка була.
sunan tauraron kuwa Maɗaci. Kashi ɗaya bisa uku na ruwaye ya zama mai ɗaci, mutane da yawa kuma suka mutu saboda shan ruwan, don ɗacinsa.
12 І четвертий ангел затрубив, і поражена стала третя часть сонця, і третя часть місяця і третя часть звізд, щоб третя часть їх затьмилась, і день щоб третю часть не сьвітив, так само й ніч.
Mala’ika na huɗu ya busa ƙahonsa, sai aka bugi kashi ɗaya bisa uku na rana, kashi ɗaya bisa uku na wata, da kashi ɗaya bisa uku na taurari, har kashi ɗaya bisa uku nasu ya duhunta. Kashi ɗaya bisa uku na yini ya kasance babu haske, haka ma kashi ɗaya bisan uku na dare.
13 І бачив я, і чув, як один ангел летів серед неба, і говорив великим голосом: Горе, горе, горе домуючим на землї від остальних голосів труби трьох ангелів, що мають трубити!
Yayinda nake kallo, sai na ji gaggafar da take tashi sama a tsakiyar sararin sama ta yi kira da babbar murya ta ce, “Kaito! Kaito! Kaiton mazaunan duniya, in an yi busan sauran ƙahonin da mala’ikun nan uku suke shirin busawa!”