< Об'явлення 5 >
1 І бачив я в правицї Сидячого на престолї книгу записану із середини і зверху, запечатану семи печатьми.
Sa’an nan na ga a hannun damar wannan wanda yake zaune a kursiyin naɗaɗɗen littafi da rubutu a ciki da wajensa an kuma hatimce shi da hatimai bakwai.
2 І бачив я ангела сильного, покликуючого голосом великим: Хто достоєн розгорнути книгу, і розломити печаті її?
Na kuma ga wani babban mala’ika yana shela da babbar murya cewa, “Wa ya cancanta yă ɓalle hatiman nan yă kuma buɗe naɗaɗɗen littafin?”
3 І нїхто не міг па небі, анї на землі, анї під землею, розгорнути книгу, анї заглянути до неї.
Amma ba wani a sama ko a ƙasa ko a ƙarƙashin ƙasan da ya iya buɗe naɗaɗɗen littafin ko ma yă duba cikinsa.
4 І я вельми плакав, що нїхто достойний не знайшов ся, щоб розгорнути і прочитати книгу, анї заглянути до неї.
Na yi ta kuka domin ba a iya samun wanda ya cancanta yă buɗe naɗaɗɗen littafin ko yă duba cikinsa ba.
5 І один із старцїв каже менї: Не плач; ось, побідив лев, що з роду Юдиного, корінь Давидів, щоб розгорнути книгу, і розломити сїм печатїй її.
Sai ɗaya daga cikin dattawan ya ce mini, “Kada ka yi kuka! Duba, Zakin kabilar Yahuda, da kuma Tushen Dawuda ya ci nasara. Ya iya buɗe naɗaɗɗen littafin da hatimansa bakwai.”
6 І поглянув я, і ось, по серединї між престолом і чотирма животними, і по серединї старцїв, стоїть Ягнятко, наче заколене, і мало сїм рогів, і сїм очей, а се сїм духів Божих, що послані по цілій землї.
Sa’an nan na ga Ɗan Rago, yana kamar an yanka, tsaye a tsakiyar kursiyin, halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan an sun kewaye shi. Yana da ƙahoni bakwai da idanu bakwai, waɗanda suke ruhohi bakwai na Allah da aka aika cikin dukan duniya.
7 І прийшов, і взяв книгу з правицї Сидячого на престолї.
Ya zo ya karɓi naɗaɗɗen littafin daga hannun dama na wannan wanda yake zaune a kursiyin.
8 І коли взяв книгу, то чотири животні і двайцять чотири старці впали перед Агнцем, маючи кожний кобзу і чашу золоту, повну пахощів, що були молитви сьвятих.
Bayan ya karɓa, sai halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan nan ashirin da huɗu suka fāɗi ƙasa a gaban Ɗan Ragon. Kowannensu yana da garaya kuma suna riƙe da kaskon zinariya cike da turare, waɗanda suke addu’o’in tsarkaka.
9 І сьпівають пісню нову, глаголючи: Достоєн єси приняти книгу, і створити печаті її, бо Ти був заколений, і відкупив єси нас Богу кровю своєю, з усякого роду, і язика, і народу і поган,
Suka rera sabuwar waƙa, “Ka cancanci ka karɓi naɗaɗɗen littafin ka kuma buɗe hatimansa, domin an kashe ka, da jininka kuma ka sayi mutane wa Allah, daga kowace kabila da harshe da mutane da kuma al’umma.
10 і зробив єси нас Богу нашому царями і священиками; і царювати мем на землї.
Ka mai da su masarauta da kuma firistoci, don su yi wa Allahnmu hidima, kuma za su yi mulki a duniya.”
11 І я бачив і чув голос ангелів многих кругом престола і животних, і старців; і було число їх тьма тьмами і тисячі тисячами,
Sai na duba na kuma ji muryar mala’iku masu yawa, yawansu kuwa ya kai dubu dubbai, da kuma dubu goma sau dubu goma. Suka kewaye kursiyin da halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan nan.
12 глаголючи голосом великим: Достоєн Агнець, заколений, приняти силу й багацтво, й премудрость, і кріпость, і честь і славу.
Da babbar murya suka rera, “Macancanci ne Ɗan Ragon nan da aka kashe, don yă sami iko da wadata da hikima da ƙarfi da girma da ɗaukaka da kuma yabo!”
13 І всяке створіннє, що в небі, і на землі, і під землею, і що на морю, і все, що в них, чув я, що говорило: Сидячому на престолі і Агнцеві благословеннє, і честь, і слава і держава по вічні віки. (aiōn )
Sa’an nan na ji kowace halitta a sama da ƙasa da ƙarƙashin ƙasa da kuma bisan teku, da kome da yake cikinsu yana rerawa, “Gare shi mai zama a kan kursiyin da kuma ga Ɗan Ragon yabo da girma da ɗaukaka da iko, (aiōn )
14 А четверо животних сказали: Амінь, а двайцять чотири старцї упали, і поклонились Живучому по вічні віки.
Sai halittu huɗun nan masu rai suka ce, “Amin”, dattawan kuma suka fāɗi suka yi sujada.