< Об'явлення 17 >

1 І прийшов один із семи ангелів, що мали сїм чаш, і говорив зо мною, глаголючи менї: Ходи, я покажу тобі суд блудницї великої, що сидить над многими водами;
Ɗaya daga cikin mala’iku bakwai masu ɗauke da kwanoni bakwai nan, ya zo ya ce mini, “Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwan nan da take zaune a bisan ruwaye masu yawa.
2 з котрою блудили парі земні, і впивались вином блудодїяння її, ті, що домують на землї.
Da ita ce sarakunan duniya suka yi zina mazaunan duniya kuma suka bugu da ruwan inabin zinace zinacenta.”
3 І повів мене духом у пустиню. І я бачив жінку, що сидїла на зьвірі кармазиновому, повному імен хули, в котрого сїм голов і десять рогів.
Sa’an nan mala’ikan ya ɗauke ni cikin Ruhu zuwa hamada. A can na ga mace zaune a kan wata jan dabbar da aka rufe da sunayen saɓo tana kuma da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
4 А жінка з'одягнена в багряницю і кармазин, і озолочена золотом, і дорогим каміннєм, і перлами, а в неї золота чаша в руцї її, повна гидоти і нечистоти блудодїяння її,
Macen tana saye da tufafi masu ruwan ja da shunayya, tana ƙyalli da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai. Tana riƙe da kwaf na zinariya a hannunta, cike da abubuwa masu banƙyama da kuma ƙazantar zinace zinacenta.
5 а на чолї її імя написане: Тайна: Вавилон великий, мати блудницям і гидотам землі.
Sunan da aka rubuta a goshinta asiri ne, Babilon mai girma mahaifiyar karuwai da kuma na abubuwa masu banƙyama na duniya.
6 І бачте я, що жінка пяна від крові сьвятих, і від крові сьвідків Ісусових; і я дивував ся, бачивши її, дивом великим.
Na ga cewa macen ta bugu da jinin tsarkaka, jinin waɗanda suka shaida Yesu. Da na gan ta, sai na yi mamaki ƙwarai.
7 І рече. менї ангел: Для чого дивуєш ся? Я тобі скажу тайну жінки, і зьвіра, що носить її, у котрого сїм голов і десять рогів:
Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Don me kake mamaki? Zan bayyana maka asirin macen nan da dabbar da take hawa, wadda take da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
8 Зьвір, котрого ти бачив, був, і вже нема його, і має він вийти з безодні, та й іти в погибіль; і будуть чудуватись домуючі на землї, (котрих імена не записані в книзі життя від основання сьвіта, ) бачивши зьвіра, що був, і нема його, хоч і єсть. (Abyssos g12)
Dabbar da ka gani, a dā ta taɓa kasancewa, a yanzu, ba ta, za tă kuma fito daga Abis zuwa ga hallakarta. Mazaunan duniya waɗanda ba a rubuta sunayensu a littafin rai tun kafin halittar duniya ba za su yi mamaki sa’ad da suka ga dabbar, domin a dā ta taɓa kasancewa, yanzu kuwa ba ta, duk da haka za tă dawo. (Abyssos g12)
9 Ось розум, в котрого мудрість. Сїм голов се сїм гір, де жінка сидить на них, і царів сїм;
“Wannan yana bukata hankali da kuma hikima. Kawuna bakwai nan tuddai bakwai ne da macen take zama a kai.
10 пять упало, а один єсть, а инший ще не прийшов; і коли прийде, то не довго має він бути.
Sarakuna bakwai ne kuma. Biyar sun fāɗi, ɗaya yana nan, ɗayan kuma bai zo ba tukuna; amma sa’ad da ya zo, zai kasance na ɗan lokaci.
11 А зьвір, котрий був, і (котрого) нема, - він восьмий, та з сїмох, і в погибіль іде.
Dabbar da a dā ta taɓa kasancewa, amma yanzu ba ta, ita ce sarki na takwas. Ita ɗaya ce cikin bakwai ɗin, kuma tana tafiya zuwa ga hallakarta.
12 А десять рогів, що бачив їх, се десять парів, котрі ще не приняли царства, тільки приймуть власть як царі, однієї години з зьвіром.
“Ƙahonin nan goma da ka gani sarakuna goma ne da ba su riga sun karɓi mulki ba, amma waɗanda na sa’a guda za su karɓi iko a matsayin sarakuna tare da dabbar.
13 Ті мають одну думку і силу, і власть свою зьвірові передадуть.
Suna da manufa guda za su kuma ba wa dabbar ikonsu da kuma sarautarsu.
14 Ті воювати муть з Агнцем, і Агнець побідить їх, бо Він Пан панів і Цар царів, а ті, що з Ним, покликані і вибрані і вірні.
Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, sai dai Ɗan Ragon zai ci nasara a bisansu domin shi ne Ubangijin iyayengiji, Sarkin sarakuna, tare da shi kuwa kirayayunsa, zaɓaɓɓunsa da kuma amintattu masu binsa za su kasance.”
15 І рече менї: Води, що ти бачив, де блудниця сидить, се люде, і громади, і народи і язики.
Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Ruwayen da ka gani, inda karuwan take zama, jama’a ce, taro masu yawa, al’ummai da kuma harsuna.
16 А десять рогів, що ти бачив на зьвірові, ті зненавидять блудницю, і спустошать її, і обнажать, і тіло її з'їдять, і спалять її в огнї.
Dabbar da kuma ƙahoni goma da ka gani za su ƙi jinin karuwar. Za su kai ta ga hallaka su kuma bar ta tsirara; za su ci namanta su kuma ƙone ta da wuta.
17 Бог бо, дав у серця їх, щоб чинили волю Його, і чинили однодушне, і дали царство своє зьвірові, доки не сповнять ся слова Божі.
Gama Allah ya sa a zukatansu su cika nufinsa ta wurin yarda su ba wa dabbar ikonsu tă yi mulki, sai lokacin da kalmomin Allah sun cika.
18 А жінка, котру ти бачив, се город великий, що має царство над царями земними.
Macen da ka gani ita ce babban birnin da yake mulki a bisan sarakunan duniya.”

< Об'явлення 17 >