< Від Матвія 27 >

1 Як же настав ранок, зробили раду всі архиєреї й старші людські
Da wayewar gari, sai dukan manyan firistoci da dattawan mutane suka yanke shawara su kashe Yesu.
2 і, звязавши Його, повели тай передали Його Понтийському Пилату, ігемонові.
Suka daure shi, suka tafi da shi, suka ba da shi ga gwamna Bilatus.
3 Тоді, побачивши Юда, зрадник Його, що Його осуджено, розкаяв ся, і вернув трийцять срібняків архиєреям та старшині,
Sa’ad da Yahuda, wanda ya bashe Yesu, ya ga an yanke wa Yesu hukuncin kisa, sai ya yi “da na sani.” Ya je mayar wa manyan firistoci da dattawan kuɗin azurfa talatin ɗin.
4 кажучи: Згрішив я, зрадивши кров невинну. Вони ж сказали: Що дам до того? ти побачиш.
Ya ce, “Na yi zunubi da na ci amanar marar laifi.” Suka ce masa, “Ina ruwanmu da wannan? Wannan dai ruwanka ne.”
5 І, покинувши він срібняки в церкві, вийшов і відійшовши, повісив ся.
Sai Yahuda ya zubar da kuɗin a cikin haikalin ya tafi. Sa’an nan ya je ya rataye kansa.
6 Архиєреї ж, взявши срібняки, сказали: Не годить ся класти їх у скарбоню, бо се ціна крові.
Manyan firistoci suka ɗauki kuɗin, suka ce, “Doka ta hana a sa kuɗin a cikin ma’aji, da yake kuɗin jini ne.”
7 Зробивши ж раду, купили за них ганчарське поле, щоб ховати на йому захожих.
Saboda haka, sai suka yanke shawara su yi amfani da kuɗin suka sayi filin mai yin tukwane, saboda binne baƙi.
8 Через се зветь ся поле се Кріваве Поле по сей день.
Shi ya sa ake kiran filin, Filin Jini har yă zuwa yau.
9 Тоді справдилось, що сказав Єремія пророк, глаголючи: І взяли вони трийцять срібняків, ціну цїненного, котрого цїнено з синів Ізраїля,
Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika cewa, “Suka ɗauki azurfa talatin, kuɗin da mutanen Isra’ila suka sa a kansa,
10 і дали їх на ганчарське поле, як повелїв менї Господь.
suka kuma yi amfani da su, suka sayi filin mai yin tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
11 Ісус же стояв перед ігемоном; і питав Його ігемон, кажучи: Чи Ти цар Жидівський? Ісус же рече йому: Ти сказав єси.
Ana cikin haka, Yesu kuwa yana tsaye a gaban gwamna, sai gwamnan ya tambaye shi, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya ce, “I, haka ne, kamar yadda ka faɗa.”
12 А, як винуватили Його архиєреї та старші, не відказував нічого.
Da manyan firistoci da dattawa suka zarge shi, bai ba da amsa ba.
13 Тоді каже до Него Пилат: Хиба не чуєш, скільки сьвідкують на Тебе?
Sai Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Ba ka jin shaidar da suke kawowa a kanka?”
14 І не відказав Він йому нї на одно слово, так що ігемон вельми дивував ся.
Amma Yesu bai ce uffam game da ko ɗaya daga cikin zargin da suka yi masa ba. Har gwamna ya yi mamaki ƙwarai.
15 На сьвято ж звик був ігемон одпускати народові одного вязника, которого вони хотіли.
A wannan irin Biki, gwamna yana da wata al’ada, ta sakin ɗan kurkuku guda wanda taron suka zaɓa.
16 Мали ж тоді знаного вязника, на прізвище Вараву.
To, a wannan lokaci kuwa suna da wani shahararren ɗan kurkuku da ake kira Barabbas.
17 Як же вони зібрались, сказав їм Пилат: Кого хочете, щоб одпустив вам: Вараву, чи Ісуса, на прізвище Христа?
Saboda haka da taron suka taru, sai Bilatus ya tambaye su ya ce, “Wane ne a cikinsu kuke so in sakar muku. Barabbas ko Yesu wanda ake kira Kiristi?”
18 Знав бо, що через зависть видали Його.
Don ya san saboda sonkai ne suka ba da Yesu a gare shi.
19 Як же сидів він на судищі, прислала до него жінка його кажучи: Нїчого тобі й праведнику сьому; багато бо терпіла я сьогоднї вві снї через него.
Yayinda Bilatus yake zaune a kan kujerar shari’a, sai matarsa ta aika masa da wannan saƙo cewa, “Kada ka sa hannunka a kan marar laifin nan, domin na sha wahala ƙwarai, a cikin mafarki yau game da shi.”
20 Архиєреї ж і старші наустили народ, щоб випросили Вараву, Ісуса ж убили.
Amma manyan firistoci da dattawa suka shawo kan taron, su ce, a ba su Barabbas, amma a kashe Yesu.
21 Озвав ся ж ігемон і рече до них: Кого хочете з двох, щоб випустив вам? Вони ж сказали: Вараву.
Gwamna ya yi tambaya ya ce, “Wane ne cikin biyun nan, kuke so in sakar muku?” Suka ce, “Barabbas.”
22 Каже до них Пилат: Що ж оце робити му з Ісусом, на призвіще Христом? Кажуть йому всі: Нехай буде рознятий.
Bilatus ya yi tambaya, “To, me zan yi da Yesu wanda ake kira Kiristi?” Duka suka ce, “A gicciye shi!”
23 Ігемон же каже: Що бо злого зробив? Вони ж кричали ще гірш: Нехай буде рознятий.
Bilatus ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara tā da ihu, suna cewa, “A gicciye shi!”
24 Бачивши ж Пилат, що нічого не врадить, а ще більш росте буча, взявши води, помив руки перед народом, і каже: Невинен я крові праведника сього; ви побачите.
Da Bilatus ya ga cewa ba ya kaiwa ko’ina, sai ma hargitsi ne yake so yă tashi, sai ya ɗibi ruwa, ya wanke hannuwansa a gaban taron ya ce, “Ni kam, ba ruwana da alhakin jinin mutumin nan. Wannan ruwanku ne!”
25 І, озвавшись увесь народ, сказав: Кров Його на нас і на діти наші.
Sai dukan mutane suka amsa, suka ce, “Bari alhakin jininsa yă zauna a kanmu da’ya’yanmu!”
26 Тоді відпустив їм Вараву; Ісуса ж, побивши, передав, щоб розпято Його.
Sai ya sakar musu Barabbas. Amma ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
27 Тоді воїни ігемонові, взявши Ісуса на судище, зібрали на Него всю роту.
Sai sojojin gwamna suka ɗauki Yesu suka kai shi Fadar mai mulki, sa’an nan suka tara dukan kamfanin sojoji kewaye da shi.
28 І, роздягнувши Його, накинули на Него червоний плащ;
Suka tuɓe shi, suka yafa masa wata jar riga.
29 і, сплівши вінець із тернини, положили на голову Йому, а тростину в правицю Його; і кидаючись на коліна перед Ним, насьміхались із Него, кажучи: Радуй ся, царю Жидівський!
Suka kuma tuƙa wani rawanin ƙaya, suka sa masa a kā. Suka sa sanda a hannun damansa. Suka durƙusa a gabansa, suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
30 І, плюючи на Него, брали тростину, й били по голові Його.
Suka tattofa masa miyau, suka karɓe sandan, suka yi ta ƙwala masa shi a kai.
31 І, як насьміялись із Него, зняли з Него плащ, і надїли на Него одежу Його, й повели Його на розпятє.
Bayan sun yi masa ba’a, sai suka tuɓe masa rigar, suka sa masa nasa tufafin. Sai suka tafi da shi, domin su gicciye shi.
32 Виходячи ж, знайшли чоловіка Киринейського, на ймя Симона; сього заставили нести хрест Його,
Suna fitowa ke nan, sai suka sadu da wani mutumin Sairin, mai suna Siman. Sai suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen.
33 І прийшовши на врочище (місце) Голгота, чи то б сказати Черепове місце,
Sai suka iso wani wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
34 дали Йому пити оцту, змішаного з жовчю; і, покуштувавши, не хотів пити.
A can, suka ba shi ruwan inabi gauraye da wani abu mai ɗaci yă sha. Amma da ya ɗanɗana, sai ya ƙi sha.
35 Розпявши ж Його, поділили одежу Його, кинувши жереб, щоб справдилось, що сказав пророк: Поділили собі шати мої, й на одежу мою кинули жереб.
Bayan da suka gicciye shi, sai suka raba tufafinsa a tsakaninsu ta wurin jefa ƙuri’a.
36 І, посідавши, стерегли Його там;
Sa’an nan suka zauna suna tsaronsa.
37 і прибили над головою Його написану вину Його: Се Ісус, цар Жидівський.
Bisa da kansa kuwa, an kafa rubutun zargin da aka yi masa, da ya ce, Wannan shi ne Yesu Sarkin Yahudawa.
38 Тодї розпято з Ним двох розбійників, одного по правицї, а другого по лївицї.
An gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗaya kuma a hagunsa.
39 Мимойдучі ж хулили Його, киваючи головами своїми,
Masu wucewa, suka zazzage shi, suna kaɗa kai,
40 і кажучи: Ти, що руйнуєш церкву, й за три днї будуєш її, спаси ся сам. Коли ти Син Божий, зійди з хреста.
suna cewa, “Kai da za ka rushe haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku, ceci kanka mana! In kai Ɗan Allah ne, ka sauka daga gicciyen!”
41 Так само ж і архиєреї, насьміхаючись із письменниками та старшими, казали:
Haka ma, manyan firistoci da malaman dokoki da kuma dattawa, suka yi ta yin masa ba’a, suna cewa,
42 Инших спасав, а себе не може спасти. Коли Він царь Ізраїлський, нехай тепер зійде з хреста, й ввіруємо в Него;
“Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa! In shi ne Sarkin Isra’ila! To, yă sauko daga kan gicciyen nan, mu kuwa mu gaskata shi.
43 Він уповав на Бога; нехай тепер визволить Його, коли хоче Його, казав бо: Я Син Божий.
Ya dogara ga Allah. Bari Allah yă cece shi yanzu, in yana sonsa, domin ya ce, ‘Ni Ɗan Allah ne.’”
44 Так само й розбійники, що були розпяті з Ним, докоряли Йому.
Haka ma,’yan fashin da aka gicciye tare da shi, suka zazzage shi.
45 Від шестої ж години настала темрява по всїй землї до години девятої.
Daga sa’a ta shida, har zuwa sa’a ta tara, duhu ya rufe ƙasa duka.
46 Коло девятої ж години покликнув Ісус великим голосом, глаголючи: Ілі, Ілі лама савахтані; те єсть: Боже мій. Боже мій, чом мене покинув єси?
Wajen sa’a ta tara, Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
47 Деякі ж, що там стояли, почувши, казали: Що Ілию кличе сей.
Sa’ad da waɗanda suke tsattsaye a wurin suka ji haka, sai suka ce, “Yana kiran Iliya.”
48 І зараз, побігши один із них, і взявши губку, сповнивши оцтом і, настромивши на тростину, поїв Його.
Nan da nan, ɗaya daga cikinsu ya ruga, ya sami soso, ya jiƙa shi da ruwan tsami, ya sa a sanda, ya miƙa wa Yesu, yă sha.
49 Останні ж казали: Нехай: побачимо, чи прийде Ілия спасати Його.
Sauran kuwa suka ce, “Ƙyale shi mu ga, ko Iliya zai zo yă cece shi.”
50 Ісус же, знов покликнувши великим голосом, зітхнув духа.
Da Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sai ya saki ruhunsa.
51 І ось завіса церковня роздерлась надвоє од верху до низу, й земля затрусилась, і скелї порозпадались;
A daidai wannan lokaci, sai labulen haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta jijjiga, duwatsu kuma suka farfashe.
52 і гроби порозкривались; і многі тіла сьвятих усопших повставали,
Kaburbura suka bubbuɗe, jikunan tsarkaka da yawa kuwa cikin waɗanda da suka mutu, suka tashi.
53 і, вийшовши з гробів після воскресення Його, поприходили у сьвятий город, і показались многим.
Suka firfito daga kaburbura, sa’an nan bayan tashin Yesu daga matattu, suka shiga birni mai tsarki, suka bayyana ga mutane da yawa.
54 Сотник же да ті, що були з ним і стерегли Ісуса, побачивши трус і те, що сталось, полякались тяжко, кажучи: Справді, Божий Син був сей.
Da jarumin nan tare da waɗanda suke tsaron Yesu, suka ga girgizar ƙasa, da kuma abin da ya faru, sai tsoro ya kama su, suka kuma ce, “Gaskiya, wannan Ɗan Allah ne!”
55 Було там багато й жінок, що оддалеки дивились, котрі прийшли слїдом за Ісусом із Галилеї, служачи Йому.
Akwai mata da yawa a can, suna kallo daga nesa. Sun bi Yesu tun daga Galili, suna masa hidima.
56 Між ними була Мария Магдалина, й Мария, мати Яковова та Йосиїна, й мати синів Зеведеєвих.
A cikinsu, akwai Maryamu Magdalin, da Maryamu uwar Yaƙub da Yoses, da kuma uwar’ya’yan Zebedi.
57 Як же настав вечір, прийшов чоловік заможний з Ариматеї, на ймя Йосиф, що й сам учив ся в Ісуса.
Da yamma ta yi, sai ga wani mutum mai arziki daga Arimateya, sunansa Yusuf, wanda shi da kansa almajirin Yesu ne.
58 Сей, приступивши до Пилата просив тіла Ісусового. Тоді Пилат і звелїв оддати тіло.
Ya je wurin Bilatus, ya roƙe shi yă ba shi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a ba shi.
59 І взявши тїло Йосиф, обгорнув його плащеницею чистою,
Yusuf ya ɗauki jikin ya nannaɗe shi da zanen lilin mai tsabta.
60 положив його у новім своїм гробі, що висік у скелї; й прикотивши великого каменя до дверей гробу одійшов.
Sa’an nan ya sa shi a sabon kabarinsa, wanda ya haƙa a dutse. Bayan ya gungura wani babban dutse ya rufe bakin kabarin, sai ya tafi abinsa.
61 Була ж там Мария Магдалина й друга Мария, і сидїли навпроти гроба.
Maryamu Magdalin da ɗayan Maryamun, suna zaune a wurin, ɗaura da kabarin.
62 Завтрішнього ж дня, що після пятницї, зібрались архиєреї та Фарисеї до Пилата,
Kashegari, wato, bayan Ranar Shirye-shirye, sai manyan firistoci da Farisiyawa, suka je wurin Bilatus.
63 кажучи: Пане, згадали ми, що той обманщик казав, ще живий: Через три днї встану.
Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun tuna, mai ruɗin nan tun yana da rai ya ce, ‘Bayan kwana uku, zan tashi daga matattu.’
64 Звели ж оце стерегти гроба до третього дня, щоб прийшовши ученики Його в ночі, не вкрали Його, й не сказали народові: Устав із мертвих; і буде остання омана гірша первої.
Saboda haka, ka ba da umarni, a tsare kabarin sai rana ta uku ɗin. In ba haka ba, almajiransa za su iya zuwa su sace jikin, sa’an nan su faɗa wa mutane cewa, an tashe shi daga matattu. Ruɗin ƙarshen nan fa, sai yă fi na farkon muni.”
65 Сказав же їм Пилат: Маєте сторожу: йдїть забезпечте, як знаєте.
Sai Bilatus ya ce, “Shi ke nan, ku ɗebi soja, ku je ku tsare kabarin iya ƙoƙarinku.”
66 Вони ж, пійшовши, забезпечили гріб, запечатавши камінь, із сторожею.
Sai suka je suka tsare kabarin ta wurin buga masa hatimi, suka kuma sa masu gadi.

< Від Матвія 27 >