< Від Матвія 26 >
1 І сталось, як скінчив Ісус, усї цї слова, рече до ученикїв своїх:
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin dukan waɗannan abubuwa, sai ya ce wa almajiransa,
2 Ви знаєте, що через два днї буде пасха, й Сина чоловічого видадуть на розпяттє.
“Kamar yadda kuka sani, Bikin Ƙetarewa sauran kwana biyu, za a kuma ba da Ɗan Mutum don a gicciye shi.”
3 Тодї зібрались архиєреї, та письменники, та старші людські у двір до архиєрея, на прізвище Каяфи,
Sai manyan firistoci da dattawan mutane, suka taru a fadan babban firist, mai suna Kayifas,
4 і радились, щоб узяти Ісуса підступом і вбити.
suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci, su kuma kashe shi.
5 Та казали: Тільки не в сьвято, щоб не було бучі між народом.
Suka ce, “Amma ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su tā da rikici.”
6 Як же був Ісус у Витанїї в господї в Симона прокаженого,
Yayinda Yesu yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu,
7 приступила да Него жінка, маючи посудинку предорогого мира, та й злила на голову Йому, як сидїв за столом.
wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tulun alabasta na turaren mai tsada sosai, wanda ta zuba a kansa a lokacin da yake cin abinci.
8 Побачивши ж ученики Його, сердились, кажучи: На що така втрата?
Sa’ad da almajiransa suka ga wannan, sai suka yi fushi. Suka ce, “Wannan almubazzaranci fa!
9 Можна бо було се миро продати дорого та дати вбогим.
Wannan turare ai, da an sayar da shi da kuɗi mai yawa a ba matalauta kuɗin.”
10 Зрозумівши ж Ісус, рече до них: що ви смутите жінку? дїло бо добре вчинила на менї.
Sane da wannan, Yesu ya ce musu, “Me ya sa kuke damun macen nan? Ta yi mini abu mai kyau ne.
11 Всякого бо часу маєте вбогих із собою, мене ж не всякого часу маєте.
Matalauta za su kasance tare da ku kullum, amma ni ba zan kasance tare da ku kullum ba.
12 Зливши бо вона миро се на тїло моє на погребеннє моє зробила.
Sa’ad da ta zuba turaren nan a jikina, ta shirya ni ne don jana’izata.
13 Істино глаголю вам: Де б нї проповідувалась євангелия ся по всьому сьвіту, казати меть ся й те, що зробила оця, на спомин її.
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bisharan nan a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”
14 Тодї, пійшовши один з дванайцятьох, на ймя Юда Іскариоцький, до архиєреїв,
Sai ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, wanda ake kira Yahuda Iskariyot, ya je wurin manyan firistoci
15 каже: Що хочете дати менї, а я вам видам Його? Вони ж поставили йому трийцять срібняків.
ya ce, “Me za ku ba ni, in na bashe shi gare ku?” Sai suka ƙirga masa kuɗi azurfa talatin.
16 І з того часу шукав нагоди, щоб Його видати.
Daga wannan lokaci, Yahuda ya yi ta neman zarafin da zai miƙa shi.
17 У первий же день опрісночний приступили ученики до Ісуса, кажучи Йому: Де хочеш, щоб приготовили Тобі їсти пасху?
A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, sai almajiran suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
18 Він же рече: Йдїть у город до оттакого, та скажіть йому: Учитель рече: Час мій близько; у тебе зроблю пасху з учениками моїми.
Ya amsa ya ce, “Ku shiga gari wurin wāne, ku ce masa, ‘Malam ya ce, lokacina ya yi kusa. Zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina a gidanka.’”
19 І зробили ученики, як повелїв їм Ісус; і приготовили пасху.
Saboda haka almajiran suka yi yadda Yesu ya umarce su, suka kuwa shirya Bikin Ƙetarewa.
20 Як же настав вечір, сїв Він за столом із дванайцятьма.
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zauna don cin abinci tare da Sha Biyun.
21 І, як вони їли, рече: Істино глаголю вам, що один з вас зрадить мене.
Yayinda suke cin abinci, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 І, засумівши тяжко, почали говорити до Него кожен з них: Аже ж не я, Господи?
Suka yi baƙin ciki ƙwarai, suka fara ce masa da ɗaya-ɗaya, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
23 Він же, озвавшись, рече: Хто вмочає зо мною руку в миску, той зрадить мене.
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya sa hannunsa a kwano tare da ni ne, zai bashe ni.
24 Син чоловічий іде, як писано про Него; горе ж чоловікові тому, що Сина чоловічого зрадить! Добре було б йому, коли б не родив ся чоловік той.
Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda aka rubuta game da shi. Amma kaiton mutumin da zai bashe Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da ya fi masa.”
25 Озвав ся ж Юда, зрадник Його, й каже: Аже ж не я, учителю? Рече до него: Ти сказав єси.
Sa’an nan Yahuda, wanda zai bashe shi ya ce, “Tabbatacce ba ni ba ne, ko, Rabbi?” Yesu ya amsa ya ce, “I, kai ma ka fada.”
26 Як же вони їли, взявши Ісус хлїб і поблагословивши, ламав, і давав ученикам, і рече: Прийміть, їжте: се єсть тїло моє.
Yayinda suke cikin cin abinci, Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya ya kuma kakkarya, ya ba wa almajiransa yana cewa, “Ku karɓa ku ci; wannan jikina ne.”
27 І, взявши чашу, й оддавши хвалу, подав їм, глаголючи: Пийте з неї всї;
Sa’an nan ya ɗauki kwaf, ya yi godiya, ya kuma ba su, yana cewa, “Ku shassha daga cikinsa, dukanku.
28 се бо єсть кров моя нового завіту, що за многих проливаєть ся на оставленнє гріхів.
Wannan jinina ne na sabon alkawari, wanda aka zubar saboda mutane da yawa, don gafarar zunubai.
29 Глаголю ж вам: Що не пити му від нинї з сього плоду винограднього аж до дня того, коли його пити му з вами новим у царстві Отця мого.
Ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabin nan ba har sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a mulkin Ubana.”
30 І засьпівавши вони, вийшли на гору Оливну.
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
31 Тодї рече до них Ісус: Всї ви поблазнитись мною сієї ночи. Писано бо: Поражу пастиря, і розсиплють ся. вівцї стада.
Sai Yesu ya ce musu, “A wannan dare, dukanku za ku ja da baya saboda ni, gama a rubuce yake cewa, “‘Zan bugi makiyayin, tumakin garken kuwa za su fasu.’
32 По воскресенню ж моїм попереджу вас у Галилею.
Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
33 Озвав ся ж Петр і каже до Него: Хоч усї поблазнять ся Тобою, я нїколи не зблазнюсь.
Bitrus ya amsa ya ce, “Ko da duka sun ja da baya saboda kai, ba zan taɓa ja da baya ba.”
34 Рече до него Ісус: Істино глаголю тобі: Що сієї ночі, перше нїж півень запіє, тричі відречеш ся мене.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya maka, a daren nan, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 Каже йому Петр: Хоч би менї з Тобою і вмерти, не відречусь Тебе. Так і всі ученики казали.
Bitrus ya furta, “Ko da ma zan mutu ne tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Dukan sauran almajiran ma suka faɗa haka.
36 Тодї приходить з ними Ісус на врочище (місце) Гетсиман, і рече до учеників: Сидїть тут, поки, пійшовши, помолюсь оттам.
Sa’an nan Yesu ya tafi da almajiransa zuwa wani wurin da ake kira Getsemane, ya ce musu, “Ku zauna nan, in je can in yi addu’a.”
37 І взяв із собою Петра та двох синів Зеведєвих, і почав скорбіти та вдаватись у тугу.
Ya ɗauki Bitrus da’ya’ya biyun nan na Zebedi tare da shi, sai ya fara baƙin ciki, ya kuma damu.
38 Тодї рече до них: Тяжко сумна, душа моя аж до смертї. Підождіть тут, і не спїте зо мною.
Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har kamar zan mutu. Ku dakata a nan, ku kuma yi tsaro tare da ni.”
39 І пройшовши трохи далїй, припав лицем своїм, молячись і глаголючи: Отче мій, коли можна, нехай мимо йде від мене чаша ся; тільки ж не як я хочу, а як Ти.
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in mai yiwuwa ne, a ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba nufina ba, sai naka.”
40 І приходить до учеників, і знаходить їх сплячих, і рече до Петра: Так не змогли ви однієї години попильнувати зо мною?
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya tarar suna barci. Ya tambayi Bitrus ya ce, “Ashe, ba za ku iya yin tsaro tare da ni ko na sa’a guda ba?
41 Пильнуйте та молїть ся, щоб не ввійшли в спокусу. Дух то охочий, тїло ж немошне.
Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
42 Знов, удруге відійшовши, молив ся, глаголючи: Отче мій, як не може ся чаша мимо йти від мене, коли не пити му її, нехай станеть ся воля твоя.
Ya sāke tafiya sau na biyu, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in ba zai yiwu a ɗauke wannan kwaf ba sai na sha shi, to, bari a aikata nufinka.”
43 І, прийшовши, знаходить їх знов сплячих, були бо очі в них важкі.
Da ya dawo, har yanzu ya tarar suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi da barci.
44 І, зоставивши їх, пійшов ізнов, і моливсь утретє, промовляючи те ж саме слово.
Saboda haka ya sāke barinsu, ya yi addu’a sau na uku, yana maimaita iri abu guda.
45 Тодї приходить до учеників своїх, і рече їм: Спіть уже й спочивайте ось настиг час, і Син чоловічий буде виданий у руки грішникам.
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya ce musu, “Har yanzu kuna barci kuna hutawa ba? Ga shi, sa’a ta yi kusa, an kuma bashe Ɗan Mutum a hannuwan masu zunubi.
46 Уставайте, ходімо: ось наближуєть ся зрадник мій.
Ku tashi, mu tafi! Ga mai bashe ni nan yana zuwa!”
47 Ще він говорив, коли се Юда, один з дванаицяти, приходить, а з ним багато народу з мечами й дручем, од архиєреїв та старших людських.
Yayinda yana cikin magana, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya iso. Tare da shi kuwa ga taro mai yawa riƙe da takuba da sanduna, manyan firistoci da dattawan mutane ne suka turo su.
48 Зрадник же Його дав знак їм, кажучи: Кого я поцїлую, той і єсть він: беріть його.
To, mai bashe shi ɗin, ya riga ya shirya alama da su, “Wanda na yi masa sumba, shi ne mutumin; ku kama shi.”
49 І, зараз приступивши до Ісуса, каже; Радуй ся, учителю; та й поцілував Його.
Da zuwansa, sai ya miƙe zuwa wurin Yesu ya ce, “Gaisuwa, Rabbi!” Sa’an nan ya yi masa sumba.
50 Ісус же рече йому: Друже, чого прийшов єси? Тодї, приступивши, наложили руки на Ісуса, та й узяли Його.
Yesu ya amsa ya ce, “Aboki, yi abin da ya kawo ka.” Sa’an nan mutanen suka matso, suka kama Yesu suka riƙe shi.
51 І ось один з тих, що з Ісусом, простягти руку, вихопив меча свого, й, вдаривши слугу архиєрейського, відтяв йому вухо.
Ganin haka, sai ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da Yesu, ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya fille masa kunne.
52 Тоді рече до него Ісус: Верни меч твій в місце його: всі бо, що візьмуть ся за меч, од меча погинуть.
Sai Yesu ya ce, masa, “Mai da takobinka kube, gama duk masu zare takobi, a takobi za su mutu.
53 Або думаєш, що не міг би нинї вблагати Отця мого, й приставив би мені більш дванайцяти легионів ангелів?
Kuna tsammani ba zan iya kira Ubana, nan take kuwa yă aiko mini fiye da rundunar mala’iku goma sha biyu ba?
54 Як же тоді справдились би писаня, що так мусить статись?
Amma ta yaya za a cika Nassin da ya ce dole haka yă faru?”
55 Тієї ж години рече Ісус до народу: Чи се як на розбійника вийшли ви з мечами та киями, брати мене? Щодня сидів я в вас, навчаючи в церкві, і не брали мене.
A wannan lokaci sai Yesu ya ce wa taron, “Ina jagoran wani tawaye ne, da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni? Kowace rana ina zama a filin haikali ina koyarwa, ba ku kuwa kama ni ba.
56 Се ж усе стало ся, щоб справдились писання пророчі. Тодї всі ученики, покинувши. Його, повтікали.
Amma wannan duka ya faru ne don a cika rubuce-rubucen annabawa.” Sa’an nan dukan almajiran suka yashe shi suka gudu.
57 Вони ж, узявши Ісуса, повели Його до Каяфи архиєрея, де письменники та старші зібрались.
Waɗanda suka kama Yesu kuwa suka kai shi wurin Kayifas, babban firist, inda malaman dokoki da dattawa suka taru.
58 Петр же йшов слїдом за Ним оддалеки до двору архиєрейського, і, ввійшовши в двір, сїв із слугами, щоб бачити конець.
Amma Bitrus ya bi daga nesa, har zuwa cikin filin gidan babban firist. Ya shiga, ya zauna tare da masu gadi, don yă ga ƙarshen abin.
59 Архиєреї ж, і старші, і вся рада шукали кривого сьвідчення на Ісуса, щоб Його вбити.
Sai manyan firistoci da’yan majalisa duka suka yi ta neman shaidar ƙarya a kan Yesu, don su sami dama su kashe shi.
60 І не знайшли. І коли багато лжесьвідків поприходило, не знайшли. Опісляж, приступивши два лжесьвідки
Amma ba su sami ko ɗaya ba, ko da yake masu shaidar ƙarya da yawa sun firfito. A ƙarshe, biyu suka zo gaba,
61 говорили: Сей казав: Я можу зруйнувати церкву Божу, й за три дні збудувати її.
suka furta cewa, “Wannan mutum ya ce, ‘Ina iya rushe haikalin Allah, in sāke gina shi cikin kwana uku.’”
62 І, вставши архиєрей, каже до Него: Нїчого не відказуєш, що сї проти Тебе сьвідкують?
Sa’an nan babban firist ya miƙe tsaye, ya ce wa Yesu, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”
63 Ісус же мовчав. І, озвавшись архиєрей, каже до Него: Заклинаю Тебе Богом живим, щоб сказав нам, чи Ти єси Христос, Син Божий?
Amma Yesu ya yi shiru. Sai babban firist ya ce masa, “Na haɗa ka da Allah mai rai. Faɗa mana in kai ne Kiristi, Ɗan Allah.”
64 Рече йому Ісус: Ти сказав єси. Тільки ж глаголю вам: Від нині побачите Сина чоловічого, по правицї сили, й грядущого на хмарах небесних.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake yadda ka faɗa. Sai dai ina gaya muku duka, nan gaba, za ku ga Ɗan Mutum zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a kan gizagizan sama.”
65 Тоді архиєрей роздер одежу свого, кажучи: Ось сказав хулу; на що нам, іще сьвідків? Ось тепер чули хулу Його;
Sa’an nan babban firist ya yage tufafinsa ya ce, “Ya yi saɓo! Don me muke bukatar ƙarin shaidu? Ga shi, yanzu kun dai ji saɓon.
66 як вам здаєть ся? Вони ж, озвавшись, сказали: Винен єсть смерти.
Me kuka gani?” Suka amsa, suka ce, “Ya cancanci mutuwa.”
67 Тоді плювали в лице Йому, й били по щоках Його, і знущались із Него,
Sai suka tottofa masa miyau a fuskarsa, suka kuma bubbuge shi da hannuwansu. Waɗansu kuma suka mammare shi
68 кажучи: Проречи нам, Христе, хто се вдарив Тебе?
suka ce, “Yi mana annabci, Kiristi. Wa ya buge ka?”
69 Петр же знадвору сидів у дворі, І приступила до него одна дівчина, кажучи: І ти був з Ісусом Галилейським.
To, Bitrus yana nan zaune a filin, sai wata yarinya baiwa, ta zo wurinsa. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu mutumin Galili.”
70 Він же відрік ся перед усіма, кажучи: Не знаю, що говориш.
Amma ya yi mūsu a gabansu duka. Ya ce, “Ban san abin da kike magana ba.”
71 Як же вийшов він до воріт, побачила його друга, та й каже до тих, що там були: І сей був з Ісусом Назарейським.
Sa’an nan ya fito zuwa hanyar shiga, inda wata yarinya kuma ta gan shi, ta ce wa mutanen da suke can, “Wannan mutum ma yana tare da Yesu Banazare.”
72 І знов одрік ся він, кленучись: Що не знаю чоловіка.
Ya sāke mūsu har da rantsuwa, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan ba!”
73 Трохи ж згодом, приступивши ті, що стояли, кажуть Петрові: Справді й ти єси з них, бо й твоя говірка виявляє тебе.
Bayan ɗan lokaci, sai na tsattsaye a wurin, suka hauro wurin Bitrus, suka ce, “Tabbatacce, kai ɗayansu ne, don harshen maganarka, ya tone ka.”
74 Тодї почав він проклинатись та, клястись: Що не знаю чоловіка. І зараз півень запіяв.
Sai ya fara la’antar kansa, yana ta rantsuwa yana ce musu, “Ban ma san mutumin nan ba!” Nan da take, sai zakara ya yi cara.
75 І згадав Петр слово Ісуса, промовлене до него: Що перше ніж півень запіе, тричі відречеш ся мене. І, вийшовши геть, плакав гірко.
Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi cewa, “Kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sani na sau uku.” Sai ya fita waje, ya yi ta kuka.