< Від Матвія 23 >
1 Рече тодї Ісус до народу, та до учеників своїх:
Sa’an nan Yesu ya ce wa taron mutane da kuma almajiransa,
2 глаголючи: На Мойсейових сїдалищах посїдали письменники та Фарисеї.
“Malaman dokoki da Farisiyawa suke zama a kujerar Musa.
3 Тим усе, що скажуть вам держати, держіть і робіть; по ділам же їх не робіть: говорять бо, й не роблять.
Saboda haka dole ku yi musu biyayya, ku kuma yi duk abin da suka faɗa muku. Sai dai kada ku yi abin da suke yi, gama ba sa yin abin da suke wa’azi.
4 Вяжуть бо тяжкі оберемки, що важко носити, й кладуть людям на плечі; самі ж і пальцем своїм не хочуть двигнути їх.
Sukan ɗaura kaya masu nauyi, su sa wa mutane a kafaɗa. Amma su kansu, ba sa ko sa yatsa su taimaka.
5 Усї ж дїла свої роблять, щоб бачили їх люде: ширять Филактериї свої, й побільшують поли в одежі своїй,
“Kome suke yi, suna yi ne don mutane su gani. Sukan yi layunsufantam-fantam bakin rigunarsu kuma sukan kai har ƙasa;
6 і люблять перші місця на бенкетах, і перші сідання по школах,
suna son wurin zaman manya a wurin biki, da kuma wuraren zama gaba-gaba a majami’u;
7 і витання на торгах, і щоб звали їх люде: Учителю, учителю.
suna so a yi ta gaisuwarsu a kasuwa, ana kuma riƙa ce musu, ‘Rabbi.’
8 Ви ж не зовіть ся учителями, один бо ваш учитель - Христос; усї ж ви брати.
“Amma kada a kira ku ‘Rabbi,’ gama kuna da Maigida ɗaya ne, ku duka kuwa,’yan’uwa ne.
9 І отця не звіть собі на землї, один бо Отець у вас, що на небі.
Kada kuma ku kira wani a duniya ‘uba,’ gama kuna da Uba ɗaya ne, yana kuwa a sama.
10 І не звіть ся наставниками, один бо в вас наставник - Христос.
Ba kuwa za a kira ku ‘malam’ ba, gama kuna da Malami ɗaya ne, Kiristi.
11 Більший же між вами нехай буде вам слугою.
Mafi girma a cikinku, zai zama bawanku.
12 Хто ж нести меть ся вгору, принизить ся, а хто принизить ся, пійде вгору.
Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi, duk kuma wanda ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.
13 Горе ж вам, письменники та Фарисеї, лицеміри! що зачиняєте царство небесне перед людми; ви бо не входите, й тих, що входять, не пускаєте ввійти.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, ku munafukai! Kun rufe ƙofar mulkin sama a gaban mutane. Ku kanku ba ku shiga ba, ba kuwa bar waɗanda suke ƙoƙarin shiga su shiga ba.
14 Горе вам, письменники та Фарисеї, лицеміри! що жерете доми вдовиць, й задля виду довго молитесь; тим ще тяжчий приймете осуд.
15 Горе вам, письменники та Фарисеї, лицеміри! що проходите море й землю, щоб зробити одного нововірця, і коли станеть ся, робите його сином пекла, удвоє гіршим вас. (Geenna )
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi tafiye-tafiye zuwa ƙasashe, ku ƙetare teku don ku sami mai tuba ɗaya, sa’ad da ya tuba kuwa, sai ku mai da shi ɗan wuta fiye da ku, har sau biyu. (Geenna )
16 Горе вам, проводирі слїпі, що кажете: Хто клясти меть ся церквою, нїчого; хто ж покленеть ся золотом Церковним, винуватий!
“Kaitonku, makafi jagora! Kukan ce, ‘In wani ya rantse da haikali, ba damuwa; amma in ya rantse da zinariyar haikali, sai rantsuwar ta kama shi.’
17 Дурні й слїпі: що бо більше: золото, чи церква, що осьвячує золото?
Wawaye makafi! Wanne ya fi girma, zinariyar, ko haikalin da yake tsarkake zinariyar?
18 І: Хто клясти меть ся жертівнею, нічого, хто ж покленеть ся даром, що на нїм, винуватий.
Kukan kuma ce, ‘In wani ya rantse da bagade, ba damuwa; amma in ya rantse da bayarwar da take bisansa, sai rantsuwar ta kama shi.’
19 Дурні й слїпі: що бо більше: дар, їй жертівня, що осьвячує дар?
Makafi kawai! Wanne ya fi girma, bayarwar, ko kuwa bagaden da yake tsarkake bayarwar?
20 Оце ж, хто клснеть ся жертівнею, кленсть ся нею і всїм, що зверху неї.
Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagade, ya rantse ne da bagaden tare da abin da yake bisansa.
21 І хто кленеть ся церквою, кленеть ся нею й тим, що живе в нїй.
Kuma duk wanda ya rantse da haikali, ya rantse ne da shi da kuma wanda yake zaune a cikinsa.
22 І хто кленеть ся небом, кленеть ся престолом Божим і тим, хто сидить на нїм.
Duk kuma wanda ya rantse da sama, ya rantse ne da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune a kansa.
23 Горе вам, письменппки та Фарисеї, лицеміри! що даєте десятину з мяти, й кропу, й кмину, а залишили важнїще в законї: суд, і милость, і віру. Се повинні були робити, да й того не залишати.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan ba da kashi ɗaya bisa goma na kayan yajinku, na’ana’a, anise, da lafsur. Amma kun ƙyale abubuwan da suka fi girma na dokoki, adalci, jinƙai da aminci. Waɗannan ne ya kamata da kun kiyaye ba tare da kun ƙyale sauran ba.
24 Проводпрі слїпі, що відціджуєте комара, верблюда ж глитаєте.
Makafi jagora! Kukan tace ƙwaro ɗan mitsil amma sai ku haɗiye raƙumi.
25 Горе вам, письменники та Фарисеї, лицеміри! що очищаєте зверху чашу й блюдо, у серединї ж повні вони здирства та неправди.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan wanke bayan kwaf da kwano, amma a ciki, cike suke da zalunci da sonkai.
26 Фарисею слїпий, очисти перш середину чаші й блюда, щоб і верх їх став ся чистий.
Kai makaho Bafarisiye! Ka fara wanke cikin kwaf da kwano, sa’an nan bayan ma zai zama da tsabta.
27 Горе вам, письменники та Фарисеї, лицеміри! що подобитесь гробам побіляним, що зверху являють ся гарними, в середині ж повні кісток мертвих і всякої нечисти.
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kuna kama da kaburburan da aka shafa musu farin fenti, waɗanda suna da kyan gani a waje, amma a ciki, cike suke da ƙasusuwan matattu da kuma kowane irin abu mai ƙazanta.
28 Так і ви зверху являєтесь людям праведні, в серединї ж повні лицемірства та беззаконня.
Haka ku ma, a waje, a idon mutane, ku masu adalci ne, amma a ciki, cike kuke da munafunci da mugunta.
29 Горе вам, письменники та Фарисеї, лицеміри! що будуєте гроби пророків та украшаєте памятники праведників,
“Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan gina kaburbura don annabawa, ku kuma yi wa kaburburan mutane masu adalci ado.
30 і мовляєте: Коли б ми були за часів батьків наших, не були б спільниками їх у крові пророків.
Kuna cewa, ‘Da mun kasance a zamanin kakanninmu, ai, da ba mu haɗa hannu da su muka karkashe annabawa ba.’
31 Сим же сьвідкуєте самі на себе, що ви сини тих, що вбивали пророків.
Ta haka kuna ba da shaida a kanku cewa ku zuriyar waɗanda suka karkashe annabawa ne.
32 І ви доповнюйте міру батьків ваших.
To, sai ku ci gaba ku cikasa ayyukan da kakanninku suka fara!
33 Змії, кодло гадюче, як утїчете від суду пекельного? (Geenna )
“Ku macizai!’Ya’yan macizai! Ta yaya za ku tsere wa hukuncin jahannama ta wuta? (Geenna )
34 Тим же то ось я посилаю до вас пророків, і мудрцїв, і письменників, і одних з них повбиваєте та порозпинаєте, а инших бити мете по школах ваших, та гонити мете від города в город:
Saboda haka ina aika muku da annabawa, da masu hikima da malamai. Waɗansunsu za ku kashe ku kuma gicciye; waɗansu kuma za ku yi musu bulala a majami’unku kuna kuma binsu gari-gari.
35 щоб упала на вас уся кров праведна, пролита на землї від крові Авеля праведного до крові Захарії, сина Варахіїного, що вбили ви між церквою й жертівнею.
Ta haka alhakin jinin masu adalcin da aka zubar a duniya, tun daga jinin Habila mai adalci, zuwa jinin Zakariya ɗan Berekiya, wanda kuka kashe tsakanin haikali da bagade zai koma kanku.
36 Істино глаголю вам: Все те прийде на кодло се.
Gaskiya nake gaya muku, duk wannan zai auko wa wannan zamani.
37 Єрусалиме, Єрусалиме, що повбивав єси пророків, і покаменував посланих до тебе! скільки раз хотів я зібрати дітей твоїх, як курка збирав курчат своїх під крила, й не схотїли!
“Urushalima, ayya Urushalima, ke da kike kashe annabawa, kike kuma jifan waɗanda aka aiko gare ki, sau da sau na so in tattara’ya’yanki wuri ɗaya, yadda kaza takan tattara’ya’yanta cikin fikafikanta, amma kuka ƙi.
38 Оце ж оставляєть ся вам дом ваш пустий.
Ga shi, an bar muku gidanku a yashe.
39 Глаголю бо вам: Не побачите мене від нинї, аж поки скажете: Благословенyyy в імя Господнє!
Gama ina gaya muku, ba za ku sāke ganina ba sai kun ce, ‘Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji.’”