< Від Матвія 14 >

1 Того часу Ірод четверовластник почув чутку про Ісуса,
A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
2 і рече до слуг своїх: Се Йоан Хреститель; він устав з мертвих, то й чудеса дїють ся від него,
sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”
3 Бо Ірод піймав був Йоана, звязав його, і вкинув у темницю за Іродияду, жінку брата свого Филипа.
To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus,
4 Бо казав йому Иоан: Не годить ся тобі мати її.
gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.”
5 І, хотїв його стратити, та опасувась народу; бо мали його за пророка.
Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.
6 У день же родин Іродових, дочка Іродиядвна танцювала перед ними й догодила Іродові.
A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai,
7 За се обіцяв він, клянучись, що дасть їй, чого просити ме.
har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
8 Вона ж, наперед навчена від матері: Дай менї, каже, тут на блюдї голову Иоана Хрестителя.
Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.”
9 І засумів Ірод; однак, задля клятьби й задля тих, що сиділи з ним за столом, звелїв дати.
Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa
10 І, пославши, стяв Йоана в темниці.
ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku.
11 І принесено голову його на блюдї, й дано дївчинї, вона ж віднесла матері своїй.
Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta.
12 І прийшли ученики його, і взяли тїло, й поховали його, й прийшовши, сповістили Ісуса.
Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.
13 Почувши про се Ісус, поплив звідтіля човном у пустиню сам один; і почувши народ, піишов слідом за Ним пішки з городів.
Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa.
14 І, вийшовши Ісус, побачив багато народу, й жалкував над ними, й сцїлив недужих їх.
Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.
15 Як же настав вечір, приступили до Него ученики Його, говорячи: Тут пустиня, і час уже минув; відошли народ, нехай іде в села, та накупить харчі собі.
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
16 Ісус же рече їм: Не треба їм ійти; дайте ви їм їсти.
Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
17 Вони ж кажуть Йому: Не маємо тут, як тільки пять хлїбів та дві рибі.
Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
18 Він же рече: Принесіть менї їх сюди.
Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
19 І звелїв народові посідати на траві, і, взявши пять хлїбів та дві рибі, й поглянувши на небо, поблагословив, і, ламлючи, подавав хлїби ученикам, а ученики людям.
Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane.
20 І їли вони всї, й понаїдались; і назбирали окрушин, що позоставались, дванайцять повних кошів.
Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
21 А тих, що їли, було тисяч із пять чоловіка, опріч жінок та дітей.
Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.
22 І примусив зараз Ісус учеників своїх увійти в човен, і плисти поперед Него на той бік, поки Він одпустить народ.
Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron.
23 А відпустивши народ, зійшов на гору самотою молитись; і як настав вечір, був там один.
Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai,
24 Човен же був уже серед моря, і било його филями; бо вітер був противний.
jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.
25 У четверту ж сторожу ночи, прийшов до них Ісус, ідучи по морю.
Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin.
26 І побачивши ученики, що Він іде по морю, стрівожились, кажучи, що се мара, й кричали з переляку.
Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”
27 Ісус же заговорив зараз до них, глаголючи: Спокойте ся: се я: не лякайтесь.
Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
28 Петр же, озвавшись, каже до Него: Господи, коли се Ти, зведи менї йти то Тебе по водї.
Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”
29 Він же рече: Іди. І вийшов Петр із човна, й пійшов по водї, щоб ійти до Ісуса.
Ya ce, “Zo.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu.
30 Та, бачивши сильний вітер, злякавсь, і, почавши тонути, кричав, говорячи: Господи, спаси мене.
Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
31 Ісус же простяг зараз руку, вхопив його, й рече до него: Маловіре, чого всумнив ся єси?
Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”
32 І як увійшли вони в човен, утих вітер.
Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta.
33 А ті, що були в човнї, приступивши, поклонились Йому, кажучи: Істино Божий Син єси.
Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”
34 І, попливши, прибули вони в землю Генисарецьку.
Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret.
35 І дознавши Його тамешні люде, послали по всій тій околиці, і приводили до Него всіх недужих;
Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu
36 і благали Його, щоб тільки приторкнутись їм до краю одежі Його; й скільки їх доторкувалось, одужували.
suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.

< Від Матвія 14 >