< Від Марка 6 >

1 І вийшовши звідтіля, прибув у свою країну; і йшли слідом за Ним ученики Його.
Yesu ya tashi daga can ya tafi garinsa, tare da almajiransa.
2 І, як настала субота, почав у школї навчати; й многі, слухаючи, дивувались, кажучи: Звідкіля се в Него? і що се за розум, даний Йому, що дива такі руками Його роблять ся?
Da Asabbaci ya kewayo, sai ya fara koyarwa a cikin majami’a, mutane da yawa da suka saurare shi, suka yi mamaki. Suna tambaya, “Ina mutumin nan ya sami waɗannan abubuwa? Wace hikima ce wannan da aka ba shi, har da yana yin ayyukan banmamaki haka!
3 Хиба ж сей не тесля, син Мариї, брат Яковів, і Йосиїв, і Юдин, і Симонів? і хиба не тут між нами сестри Його? І поблазнились Ним.
Ashe, wannan ba shi ne kafinta nan ba? Shin, ba shi ne ɗan Maryamu ba, ba shi ne ɗan’uwan su Yaƙub, Yusuf, Yahuda da kuma Siman ba? Ashe,’yan’uwansa mata kuma ba suna nan tare da mu ba?” Sai suka ji haushinsa.
4 Рече ж їм Ісус: Не єсть пророк без чести, хиба що в країні своїй, та в родині, і в домівці своїй.
Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa kaɗai, da kuma cikin’yan’uwansa, da cikin gidansa ne, annabi ba shi da daraja.”
5 І не міг там ніякого чуда зробити, тільки на деяких недужих положивши руки, сцїлив їх.
Bai iya yin ayyukan banmamaki a wurin ba, sai dai ɗibiya hannuwansa da ya yi a kan mutane kima da suke da cututtuka, ya kuwa warkar da su.
6 І дивувавсь недовірством їх. І ходив кругом по селах, навчаючи.
Ya kuwa yi mamaki ƙwarai don rashin bangaskiyarsu. Sai ya Yesu zazzaga ƙauyuka yana koyarwa.
7 І покликав дванайцятьох, та й почав їх посилати по двоє, і дав їм власть над духами нечистими;
Ya kira Sha Biyun nan wurinsa, ya aike su biyu-biyu, ya kuma ba su iko bisa mugayen ruhohi.
8 і звелїв їм, щоб нічого не брали на дорогу, тільки одну палицю: ні торбини, нї хліба, ні у черес грошей,
Ga dai umarnansa, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, sai dai sanda ba burodi, ba jaka, ba kuɗi a ɗamararku.
9 щоб обувались у постоли й не вдягались у дві одежині.
Ku sa takalma, amma ban da riga fiye da waɗanda kuka sa.
10 І рече їм: Де б ви нї зайшли в яку господу, там пробувайте, аж поки вийдете звідтіля.
Duk sa’ad da kuka shiga wani gida, ku zauna nan sai kun bar garin.
11 А хто не прийме вас, анї слухати ме вас, то, виходячи звідтіля, обтрусіть і порох із під ніг ваших, на сьвідкуваннє їм. Істино глаголю вам: Одраднїще буде Содомові та Гоморі суднього дня, ніж городові тому.
In kuwa a wani wuri ba a karɓe ku, ba a kuwa saurare ku ba, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita, a matsayin shaida a kansu.”
12 І вийшовши вони, проповідували, щоб каялись.
Suka fita, suna yi wa’azi, suna ce wa mutane su tuba.
13 І бісів багато виганяли, й намащували оливою багато недужих, і сцїляли.
Suka fitar da aljanu da yawa, suka shafa wa marasa lafiya da yawa mai, suka kuwa warkar da su.
14 І дочувся цар Ірод (явне бо зробилось імя Його), і каже: Що Йоан Хреститель із мертвих устав, і того роблять ся чудеса від него.
Sarki Hiridus ya ji wannan labari, gama sunan Yesu ya bazu a ko’ina. Waɗansu suna cewa, “An tashe Yohanna Mai Baftisma daga matattu ne, shi ya sa yana da ikon yin ayyukan banmamakin nan.”
15 Инші казали, що се Ілия; инші ж казали, що се пророк або один з пророків.
Waɗansu suka ce, “Ai, Iliya ne.” Har wa yau waɗansu suka ce, “Ai, annabi ne, kamar ɗaya daga cikin annabawan dā.”
16 Почувши ж Ірод, сказав: Що се Йоан, котрого я стяв, він устав з мертвих.
Amma da Hiridus ya ji haka, sai ya ce, “Ai, Yohanna ne, mutumin da na yanke masa kai, shi ne ya tashi daga matattu!”
17 Сей бо Ірод, піславши, взяв Йоана, та й звязав його в темниці за Іродияду, жінку Филипа, брата свого; бо оженивсь із нею.
Gama Hiridus da kansa ya ba da umarni a kama Yohanna, ya kuma sa aka daure shi, aka sa shi a kurkuku. Ya yi haka saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus, wadda ya aura.
18 Сказав бо Иоан Іродові: Що не годить ся тобі мати жінку брата твого.
Gama Yohanna ya yi ta ce wa Hiridus, “Ba daidai ba ne bisa ga doka, ka ɗauki matar ɗan’uwanka.”
19 Іродияда ж лютувала на него, й, хотіла його вбити, та не могла.
Saboda haka, Hiridiyas ta ƙulla munafunci game da Yohanna, ta kuma so ta kashe shi. Amma ba tă iya ba,
20 Ірод бо боявсь Иоана, знавши його, яко чоловіка праведного й сьвятого, то й беріг його й, слухаючи його, багато робив, і залюбки його слухав.
domin Hiridus yana jin tsoron Yohanna, ya kuma kāre shi sosai, da sanin cewa shi mutum ne mai adalci da kuma mai tsarki. Duk sa’ad da Hiridus ya saurari Yohanna, yakan damu ƙwarai, duk da haka, yakan so yă ji shi.
21 Як же настав день нагідний, кали Ірод на свої родини бенкет справив дукам своїм, та гетьманам, та значним Галилейським,
A ƙarshe, ta sami zarafi. A ranar murnar haihuwar Hiridus, ya yi biki domin hakimansa, da shugabannin sojojinsa, da kuma manyan mutanen Galili.
22 і як увійшла дочка тієї Іродияди, танцювала, й догодила Іродові, й, тим, що сиділи з ним, озвав ся цар до дївицї: Проси в мене, чого бажаєш, а дам тобі.
Sa’ad da diyar Hiridiyas ta shigo, ta kuma yi rawa, sai ta gamshi Hiridus tare da baƙinsa. Sai Sarkin ya ce wa yarinyar, “Ki tambaye ni kome da kike so, ni kuwa zan ba ki.”
23 І поклявсь їй: Що, чого б у мене нї попросила, дам тобі, хочби й половину царства мого.
Ya yi mata alkawari da rantsuwa cewa, “Duk abin da kika roƙa, zan ba ki, ko da rabin mulkina ne.”
24 Вона ж, вийшовши, каже матері своїй: Чого просити? Та ж каже: Голови Йоана Хрестителя.
Sai ta fita ta ce wa mahaifiyarta, “Me zan roƙa?” Ta ce, “Kan Yohanna Mai Baftisma.”
25 І, ввійшовши зараз швидко до царя, просила, кажучи: Хочу, шоб менї дав зараз на блюді голову Йоана Хрестителя.
Nan da nan, sai yarinyar ta yi hanzari zuwa wajen sarki da roƙon, “Ina so ka ba ni kan Yohanna Mai Baftisma a cikin tasa, yanzu-yanzu nan.”
26 І зажурившись вельми цар, та задля клятьби й задля тих, що з ним сиділи, не хотів їй відмовити.
Sai sarki ya yi baƙin ciki ƙwarai, amma saboda rantsuwar da kuma baƙinsa, bai so yă hana ta ba.
27 І зараз піславши цар ката, звелїв принести голову його; він же пійшовши, стяв його в темниці.
Nan take, sai ya aiki mai aiwatar da kisa da umarni ya kawo kan Yohanna. Mutumin ya je ya yanke kan Yohanna a kurkuku.
28 І приніс голову його на блюдї, і дав її дівиці, а дївиця дала її матері своїй.
Ya kuma kawo kan a tasa ya ba yarinyar. Ita kuma ta ba wa mahaifiyarta.
29 І, довідавшись ученики його, пійшли і взяли тіло його, та й положили його в гробі.
Da almajiran Yohanna suka sami labari, sai suka zo suka ɗauki jikinsa suka binne a kabari.
30 І посходились апостоли до Ісуса, й сповістили Його про все, й що робили, й чого навчали.
Manzannin suka taru kewaye da Yesu, suka ba shi rahoton duk abin da suka yi, da kuma suka koyar.
31 І рече до них: Ійдїть ви самі окроме в пусте місце, та відпочиньте трохи; було бо багато, що приходили й відходили, й навіть ніколи було їм їсти.
To, saboda mutane da yawa suna kai da kawowa, har ma ba su sami damar cin abinci ba, sai ya ce musu, “Ku zo mu kaɗaita inda ba kowa don ku ɗan huta.”
32 І поплили в пусте місце човном, окроме.
Sai suka tafi a jirgin ruwa su kaɗai, inda ba kowa.
33 І бачив їх народ, як відчалювали, й пізнали Його многі, і збігались туди пішки з усіх городів, та й випередили їх, і посходились до Него.
Amma mutane da yawa waɗanda suka ga tashinsu, sun gane su, sai suka ruga da gudu a ƙafa daga dukan birane, suka riga su kaiwa can.
34 І вийшовши Ісус, побачив багато народу, й жалкував над ними, що були як вівці, не маючі пастиря, і почав навчати їх багато.
Da Yesu ya sauka, ya ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu, gama kamar tumaki suke waɗanda ba su da makiyayi. Sai ya fara koya musu abubuwa da yawa.
35 І як уже багато часу минуло, приступивши до Него ученики Його, кажуть: Що се пусте місце, і вже час пізний, -
A lokacin nan yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce masa, “Wurin nan ƙauye ne, ga shi kuma lokaci ya ƙure.
36 відпусти їх, щоб, пійшовши по околичнїх хуторах та селах, купили собі хлїба: не мають бо що їсти.
Ka sallami mutanen su shiga ƙauyukan da suke kurkusa, su sayi wa kansu wani abu, su ci.”
37 Він же, озвавшись, рече до них: Дайте ви їм їсти. І кажуть Йому: Хиба, пійшовши, купимо за двістї денариїв хлїба, й дамо їм їсти?
Sai ya amsa ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Suka ce masa, “Ai, wannan zai ɗauki albashin wata takwas na mutum! Mu je mu kashe yawan kuɗin nan a burodi mu ba su su ci?”
38 Він же рече до них: Скільки хлїбів маєте? йдїть та подивіть ся. І, взнавши, кажуть: Пять, та дві рибі.
Sai ya yi tambaya ya ce, “Burodi nawa kuke da su? Je ku duba.” Da suka duba, sai suka ce, “Biyar da kifi biyu.”
39 І звелів їм садовити всіх купа коло купи на зеленій траві,
Sa’an nan Yesu ya umarce su su sa dukan mutanen su zazzauna ƙungiya-ƙungiya a kan ɗanyar ciyawa.
40 і посідали вони ряд коло ряду по сотням і по півсотням.
Haka suka zazzauna a ƙungiyar ɗari-ɗari, da kuma hamsin-hamsin.
41 І, взявши пять хлїбів та дві рибі, й поглянувши на небо, благословив, і ламав хлїби, та й давав ученикам своїм, щоб клали перед ними; й дві рибі поділив усїм.
Ya ɗauki burodi guda biyar da kifin nan biyu, ya ɗaga kai sama, ya yi godiya, ya kakkarya burodin. Sai ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutane. Ya kuma rarraba kifi biyun a tsakaninsu duka.
42 І їли всі, й наситились.
Kowa ya ci, ya ƙoshi,
43 І набрали окрушин дванайцять повних кошів, та й із риб.
almajiran suka kwashe gutsattsarin burodin da na kifin cike da kwanduna goma sha biyu.
44 А тих, що їли хлїби, було з пять тисяч чоловіка.
Yawan mutanen da suka ci kuwa maza dubu biyar ne.
45 І зараз примусив учеників своїх увійти в човен, та плисти на той бік попереду 'д Витсаїдї, поки сам одпустить народ.
Nan da nan Yesu ya sa almajiransa su shiga jirgin ruwa, su sha gabansa zuwa Betsaida, shi kuma yă sallami taron.
46 І, відпустивши їх, пійшов на гору молитись.
Bayan ya bar su, sai ya hau kan dutse don yă yi addu’a.
47 І як настав вечір, був човен серед моря, а він один на землі.
Da yamma ta yi, jirgin ruwan yana tsakiyar tafkin, Yesu kuma yana can a ƙasa shi kaɗai.
48 І бачив, як вони силкувались, веслуючи; був бо вітер противний їм; і коло четвертої сторожи ночі приходить до них, ідучи по морю, і хотів минути їх.
Ya ga almajiran suna fama da tuƙi saboda iska tana gāba da su. Wajen tsara ta huɗu na dare, sai ya tafi wurinsu, yana takawa a kan tafkin. Ya yi kamar zai wuce su,
49 Вони ж, бачивши Його, що ходить по морю, думали, що се мара, та й закричали:
amma da suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai suka yi tsammani fatalwa ce. Sai suka yi ihu,
50 всі бо Його бачили, й потрівожились. І зараз заговорив до них, і рече їм: Бодріть ся; се я; не лякайтесь.
domin dukansu sun gan shi, suka kuma tsorata. Nan da nan ya yi magana da su ya ce, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
51 І ввійшов до них у човен; і втих вітер, і вельми, над міру здумілись у собі, і дивувались.
Sai ya shiga jirgin ruwan tare da su, iskar kuma ta kwanta. Dukansu suka yi mamaki,
52 Не зрозуміли бо про хлїби: було бо серце їх засліплене.
gama ba su fahimci al’amarin burodin nan ba, don zuciyarsu ta taurare.
53 І, перепливши, прибули в землю Генисарецьку, й причалили.
Da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret, suka daure jirgin a ƙugiya.
54 І як вийшли вони з човна, зараз, пізнавши Його,
Da fitowarsu daga jirgin, sai mutane suka gane Yesu.
55 кинулись по всій тій околиці, та й почади приносити на ношах тих, що нездужали, як почули, що Він там єсть.
Suka gama yankin da gudu, suna ɗaukan marasa lafiya a kan tabarmai zuwa duk inda suka ji yake.
56 І куди нї приходив Він, у села, чи городи, чи хутори, на майданах клали недужих, і благали Його, щоб їм хоч до краю одежі Його приторкнутись, і хто тільки доторкнувсь Його, спасав ся.
Duk inda ya shiga, cikin ƙauyuka, birane ko karkara, sai su kwantar da marasa lafiya a bakin kasuwa. Suka roƙe shi yă bari su taɓa gefen rigarsa kawai, kuma duk waɗanda suka taɓa shi kuwa, suka warke.

< Від Марка 6 >