< Від Марка 3 >

1 І ввійшов ізнов у школу; й був там чоловік, що мав суху руку.
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 І назирали Його, чи сцїлить його в суботу, щоб обвинуватити Його.
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 І рече до сухорукого чоловіка: Стань посередині.
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 І рече до них: Чи годить ся в суботу добро робити, чи зло робити? життє спасати, чи погубляти? Вони ж мовчали.
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 І, позирнувши на них кругом гнівно, жалкуючи над скаменїлостю сердець їх, рехе чоловікові: Простягни руку твою. І простяг, і стала рука його здорова, як і друга.
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 І вийшовши Фарисеї, зараз з Iродиянами зробили раду на Него, як Його погубити.
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 Ісус же відійшов з учениками своїми до моря; а великий натовп із Галилеї йшов за Ним, і з Юдеї,
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 і з Єрусалиму, й з Ідумеї, і зза Йордану; й ті, що кругом Тира та Сидона, натовп великий, прочувши, скільки Він робив, поприходили до Него.
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 І сказав Він ученикам своїм наготовити Йому човна задля народу щоб не тиснулись до Него.
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 Многих бо сцїлив, так що видались на Него, щоб приторкнутись до Него, хто з них мав недуги.
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 А духи нечисті, як бачили Його то падали ниць перед Ним, і кричали, говорячи: Ти єси Син Божий.
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 І остро грозив їм, щоб Його не виявляли.
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 І вийшов Він на гору, й покликав, кого схотів сам, і поприходили до Него.
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 І настановив дванайцятьох, щоб були з Ним, і щоб посилати їх проповідувати,
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 і щоб мали силу сцїляти недуги, й виганяти біси.
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 І дав Симонові імя Петр;
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 та Якова Зеведеєвого, та Йоана, брата Якового, й дав їм імена Воанер-гес, що єсть: Сини громові;
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 та Андрея, та Филипа, та Вартоломея, та Маттея, та Тому, та Якова Алфєєвого, та Тадея, та Симона Хананця,
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 та Юду Іскариодького, що зрадив Його.
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 Входять вони в господу, і знов сходить ся народ, так що не могли анї хлїба з'їсти.
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 І прочувши свояки Його, вийшли взяти Його; казали бо, що Він не при собі.
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 А письменники, поприходивши з Єрусалиму, казали, що Вельзевула має, і що бісовським князем виганяє біси.
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 І, покликавши їх, говорив до них приповістями: Як може сатана сатану виганяти?
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 І коли царство проти себе роздїлить ся, не може стояти царство те.
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 І коли господа проти себе роздїлить ся, не може стояти господа тая.
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 І коли сатана устав проти себе, й розділив ся, не може стояти, а копець йому.
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 Не може нїхто надоби сильного, ввійшовши в господу його, пожакувати, як перше сильного не звяже; аж тодї господу його пограбить.
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 Істино глаголю вам: Що всї гріхи відпустять ся синам чоловічим, і хули, якими б вони нї хулили;
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 хто ж хулити ме на Духа сьвятого, не має прощення во віки, а винен вічного осуду: (aiōn g165, aiōnios g166)
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 бо казали: Духа нечистого має.
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 Приходять тодї брати й мати його, й стоячи на дворі, послали до Него, кличучи Його.
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 І сидїв народ круг Него; кажуть же Йому: Ось мати Твоя і брати Твої на дворі шукають Тебе.
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 І, озвавшись до них, рече: Хто се мати моя, або брати мої?
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 І, позирнувши кругом по тих, що сидїли коло Него, рече: Оце мати моя, і брати мої!
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 Хто бо чинити ме волю Божу, той брат менї, й сестра моя, і мати.
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”

< Від Марка 3 >