< Від Луки 17 >
1 Рече ж до учеників: Не можна не прийти поблазням; горе ж, через кого приходять!
Yesu ya ce wa almajiransa, “Dole ne a sami abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi, amma kaiton mutumin nan wanda suke zuwa ta wurinsa.
2 Лучче б йому було, коли б жорно млинове почеплено на шию йому, та й укинуто в море, нїж щоб зблазнив одного з малих сих.
Gwamma a ɗaura dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku, da ya sa ɗaya daga cikin ƙananan yaran nan ya yi zunubi.
3 Озирайтесь на себе. Коли погрішить проти тебе брат твій, докори йому й коли покаєть ся, прости йому.
Saboda haka, ku lura da kanku. “In ɗan’uwanka ya yi zunubi, ka kwaɓe shi. In ya tuba, ka gafarta masa.
4 І коли сїм раз на день погрішить проти тебе, й сїм раз на день обернеть ся до тебе, кажучи: Каюсь; прости йому.
In ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, ya kuma dawo sau bakwai ɗin a wurinka, yana cewa, ‘Na tuba,’ sai ka gafarta masa.”
5 І казали апостоли Господеві: Прибав нам віри.
Sai manzannin suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya!”
6 Рече ж Господь: Коли б ви мали віру з зерно горчицї, то сказали б щовковинї оцій: Викоренись і посадись у морю, то послухала б вас.
Ya amsa musu ya ce, “In kuna da bangaskiya da take ƙanƙani kamar ƙwayar mustad, kuna iya ce wa wannan itacen durumi, ‘Ka tumɓuke daga nan, ka dasu a cikin teku.’ Zai kuwa yi muku biyayya.
7 Хто ж з вас, слугу мавши, ратая чи пастуха, як ійде з поля, скаже йому зараз: Прийшовши сїдай їсти?
“In ɗaya a cikinku yana da bawa, wanda yake masa noma, ko kiwon tumaki, da dawowar bawan daga gonar, ai, ba zai ce masa, ‘Ka zo nan, ka zauna, ka ci abinci ba’?
8 А чи не скаже йому: Наготов менї що вечеряти, та підперезавшись послугуй менї, поки їсти му та пити му, а потім їсти меш і пити меш ти?
Ashe, ba zai ce masa, ‘Ka shirya mini abincin yamma, ka shirya ka yi mini hidima domin in ci in sha, bayan haka kana iya ci, ka kuma sha ba’?
9 Чи дякує тому слузї, що зробив, що звелено йому?
Shin, zai gode wa bawan don yă yi aikin da aka ce ya yi ne?
10 Так і ви, коли зробите все, що звелено вам, кажіть: Що слуги ми нікчемні; бо, що повинні зробити, вробили.
Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’”
11 І сталось, як ійшов Він у Єрусалим, і проходив серединою Самариї та Галидеї,
Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi takan iyakar Samariya da Galili.
12 і, як увійшов ув одно село, зустріло Його десять прокажених чоловіків, що стояли оддалеки.
Da zai shiga wani ƙauye, sai maza goma da suke da kuturta suka sadu da shi. Suka tsaya da nesa,
13 І піднесли вони голос, кажучи: Ісусе, наставниче, помилуй нас.
suka yi kira da babbar murya, suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka ji tausayinmu!”
14 І побачивши рече їм: Ідїть покажіть себе священикам. І сталось, як пійшли вони, очистились.
Da ya gan su sai ya ce, “Ku je ku nuna kanku ga firistoci.” Suna kan hanyar tafiya sai suka tsabtacce.
15 Один же з них, бачивши, що одужав, вернувсь, голосом великим прославляючи Бога,
Da ɗayansu ya ga ya warke, sai ya koma, yana yabon Allah da babbar murya.
16 і, припав лицем до ніг Його, дякуючи Йому; а був він Самарянин.
Ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya gode masa. Shi kuwa mutumin Samariya ne.
17 Озвав ся ж Ісус і рече: Чи не десять очистились? девять же де?
Yesu ya yi tambaya ya ce, “Ba duka goma ne aka tsabtacce ba? Ina sauran taran?
18 Не знайшлись, щоб вернувшись оддати славу Богу, тільки чужоземець сей?
Ba wanda ya dawo don yă yabi Allah, sai dai wannan baƙon?”
19 І рече йому: Уставши йди; віра твоя спасла тебе.
Sai ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 Як же спитали Його Фарисеї, коли прийде царство Боже, відказав їм, і рече: Не прийде царство Боже з постереганнєм,
Wata rana, Farisiyawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai zo, Yesu ya amsa ya ce, “Ai, mulkin Allah ba takan zo ta wurin yin kallon ku ba.
21 анї казати муть: Дивись, ось воно; або: Дивись, он, бо царство Боже у вас усерединї.
Mutane kuma ba za su ce, ‘Ga shi nan,’ ko kuma, ‘Ga shi can’ ba, domin mulkin Allah yana cikinku ne.”
22 Рече ж де учеників: Прийдуть дні, що бажати мете один з днїв Сина чоловічого вь'дїти, та й не побачите.
Sai ya ce wa almajiransa, “Lokaci yana zuwa da za ku yi marmarin ganin rana ɗaya cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba.
23 І казати муть вам: Дивись, ось; або: Дивись, он; не йдіть і не ганяйтесь.
Mutane za su ce muku, ‘Ga shi can!’ Ko kuma, ‘Ga shi nan!’ Kada ku yi hanzarin binsu.
24 Бо, як блискавиця, блиснувши з одного краю під небом, до другого краю під небом сьвітить, так буде й Син чоловічий дня свого.
Gama Ɗan Mutum, a cikin ranarsa, zai zama kamar walƙiya da take walƙawa, da take kuma haskaka sararin sama, daga wannan kusurwa zuwa wancan kusurwa.
25 Перше ж мусить Він багато терпіти й відцураєть ся Його рід сей.
Amma da fari, dole yă sha wahaloli masu yawa, kuma mutanen zamanin nan su ƙi shi.
26 І як сталось за днїв Ноя, так буде й за днїв Сива чоловічого.
“Daidai kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a zamanin Ɗan Mutum.
27 Їли, пили, женились, оддавались, аж до дня, як увійшов Ной у ковчег, і настав потоп, та й вигубив усіх.
Mutane suna ci, suna sha, suna aurayya, ana kuma ba da su ga aure, har ranar da Nuhu ya shiga jirgin. Sa’an nan ambaliyar ruwan ya sauka, ya hallaka su duka.
28 Так само, як сталось і за Лота; їли, пили, торгували, продавали, насаджували, будували,
“Haka ma aka yi a zamanin Lot. Mutane suna ci, suna sha, suna saya, suna sayarwa, suna shuki, suna kuma gine-gine.
29 которого ж дня вийшов Лот із Содома, линуло огнем та сіркою з неба та й вигубило всіх.
Amma a ranar da Lot ya bar Sodom, sai aka yi ruwan wuta da farar wuta daga sama, aka hallaka su duka.
30 Так же буде й в день, котрого Син чоловічий відкриєть ся.
“Daidai haka zai zama, a ranar da Ɗan Mutum zai bayyana.
31 Того дня, хто буде на криші, а надібє його в хатї, нехай не злазить узяти його; й хто на полї, так само нехай не вертаєть ся назад.
A ranan nan, kada wanda yake kan rufin gidansa ya sauka don yă kwashe dukiyarsa da take cikin gidan. Haka ma duk wanda yake gona, kada yă koma don wani abu.
32 Спогадайте Лотову жінку.
Ku tuna fa da matar Lot!
33 Коли хто шукати ме душу свою спасти, погубить її, а хто погубить її, оживить її.
Duk wanda yake so ya ceci ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai cece shi.
34 Глаголю вам, тієї ночі буде двоє на однім ліжку; один візьметь ся, а другий зоставить ся.
Ina gaya muku, a daren nan, mutane biyu za su kasance a gado ɗaya, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.
35 Дві молоти муть укупі; одна візьметь ся, а друга зоставить ся.
Mata biyu za su kasance suna niƙan hatsi tare, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.”
36 Двоє будуть у полї; один візьметь ся, а другий зоставить ся.
37 І озвавшись кажуть до Него: Де, Господи? Він же рече їм: Де тїло, там збирати муть ся орли.
Suka tambaya, suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “Ai, inda gawa take, nan ne ungulai za su taru.”