< Від Луки 11 >
1 І сталось, як Він молив ся на одному місці, і як перестав, сказав один з учеників до Него: Господи, навчи нас молитись, як і Йоан навчив учеників своїх.
Wata rana Yesu yana addu’a a wani wuri. Da ya gama, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Ubangiji, ka koya mana yin addu’a, kamar yadda Yohanna ya koya wa almajiransa.”
2 Рече ж їм: Коли молитесь, кажіть: Отче наш, що на небесах! Нехай святить ся імя Твоє, нехай прийде царство Твоє, нехай буде воля Твоя, як на небі, так і на землї.
Sai ya ce musu, “Sa’ad da kuke yin addu’a ku ce, “‘Ya Uba, sunanka mai tsarki ne mulkinka ya zo.
3 Хлїб наш щоденний дай нам сьогодні.
Ka ba mu kowace rana abincin yini.
4 І прости нам довги наші, як і ми прощаємо кожному довжникові нашому; й не введи нас у спокусу, а ізбави нас од лукавого.
Ka gafarta mana zunubanmu, kamar yadda mu ma ke gafarta wa duk wanda ya yi mana laifi. Kada ka bari a kai mu cikin jarraba.’”
5 І рече до них: Хто з вас мати ме приятеля, і прийде до него о півночі, і скаже йому: Друже, позич менї три хліби,
Sa’an nan ya ce musu, “Da a ce ɗayanku yana da aboki, sa’an nan ya je wurinsa da tsakar dare ya ce, ‘Aboki, ranta mini burodi guda uku,
6 бо приятель мій прийшов до мене з дороги, й не маю що поставити перед ним;
domin wani abokina da yake tafiya ya sauka a wurina. Ga shi, ba ni da abinci da zan ba shi.’
7 а той із середини, озвавшись, скаже: Не турбуй мене; вже двері зачинені, і діти мої зо мною в постелї; не можу, вставши, дати тобі:
Sai wanda yake cikin ɗaki ya amsa ya ce, ‘Kada ka dame ni. An riga an kulle ƙofa, da ni da yarana kuwa mun kwanta, ba zan iya tashi in ba ka kome ba.’
8 глаголю вам: Хоч і не дасть йому, вставши, що він йому друг, та задля докучання його, вставши, дасть йому, скільки йому треба.
Ina gaya muku, ko da yake ba zai so ya tashi ya ba shi burodin don shi abokinsa ne ba, duk da haka, zai tashi ya ba shi yawan abin da yake bukata, saboda nacewarsa.
9 І я вам глаголю: Просїть, то й дасть ся вам; шукайте, то й знайдете; стукайте, то й одчинить ся вам.
“Don haka ina faɗa muku, ku roƙa, za a ba ku, ku nema za ku samu, ku ƙwanƙwasa za a kuwa buɗe muku ƙofa.
10 Кожен бо, хто просить, одержує; і хто шукав, знаходить; і хто стукає, тому відчиняють.
Gama duk wanda ya roƙa, yana karɓa, mai nema yana samu, wanda ya ƙwanƙwasa kuma, za a buɗe masa ƙofa.
11 У которого ж з вас, батьків, просити ме син хліба, чи каменя подасть йому? а як риби, чи замість риби гадюку подасть йому?
“Wane mahaifi ne a cikinku, in ɗansa ya roƙe shi kifi, zai ba shi maciji a maimakon,
12 Або коли просити ме яйця, чи подасть йому скорпиона?
ko kuma in ya roƙi ƙwai, ya ba shi kunama?
13 Коли ж ви, лихими бувши, знаєте добрі дари давати дїтям вашим, яв же більш Отець із неба, не дасть Духа сьвятого тим, що просять у Него?
In fa haka ne, ko da yake ku mugaye ne, kun san ba’ya’yanku kyautai masu kyau, balle fa Ubanku na sama, zai yi fiye da haka, ta wurin ba da Ruhu Mai Tsarki, ga masu roƙonsa!”
14 І вигнав біса, а той був нїмий. Стало ся ж, як диявол вийшов, промовив нїмий; і дивувавсь народ.
Sa’ad da Yesu yake fitar da wani beben aljani daga wani mutum, da aljanin ya fita, sai mutumin wanda da bebe ne, ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki.
15 Деякі ж з них казали: Вельзевулом, князем бісовським, виганяв біси.
Amma waɗansunsu suka ce, “Ai, da ikon Be’elzebub, sarkin aljanu ne, yake fitar da aljanu.”
16 Другі ж, спокушуючи Його, ознаки від Него шукали з неба.
Waɗansu kuma suka gwada shi, ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
17 Він же, знаючи думки їх, рече їм: Кожне царство, проти себе розділившись, пустіє; і господа - проти господи, падає.
Yesu kuwa ya san tunaninsu, sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa, zai lalace, kuma gidan da yake gaba da kansa zai rushe.
18 Коли ж і сатана проти себе роздїлить ся, яв устоїть царство його? Бо кажете, що Ведьзевулом виганяю біси.
In Shaiɗan yana gāba da kansa, yaya mulkinsa zai tsaya? Ina faɗin haka domin kun ce, da ikon Be’elzebub nake fitar da aljanu.
19 Коли ж я Вельзевулом виганяю біси, то сини ваші ким виганяють їх? Тим суддями вашими вони будуть.
In da ikon Be’elzebub nake fitar da su, to, da ikon wa masu binku suke fitar da su? Saboda haka, za su zama alƙalanku ke nan.
20 Коли ж пальцем Божим виганяю біси, то конче пристигло до вас царство Боже.
Amma in da ikon Allah ne ni nake fitar da aljanu, ashe, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
21 Коли ж сильний, в'оружившись, стереже свого двору, то в спокою добро його.
“Sa’ad da mutum mai ƙarfi, wanda yake da makamai yana gadin gidan kansa, an tsare lafiyar dukiyarsa ke nan.
22 Коли ж сильнїщий над него, прийшовши, подужав його, то всю зброю його бере, що на неї вповав, та й роздав здобич його.
Amma in wani wanda ya fi shi ƙarfi, ya faɗa masa ya kuma sha ƙarfinsa, yakan ƙwace makaman da mutumin ke dogara da su, ya kuma rarraba ganima.
23 Хто не зо мною, той проти мене; і хто не збирає зо мною, розсипає.
“Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni, wanda kuma ba ya tarawa da ni, watsarwa yake yi.
24 Як же нечистий дух вийде з чоловіка, то блукав по безвіддях, шукаючи впокою, і, не знайшовши, каже: Вернусь до домівки моєї, звідкіля вийшов.
“Lokacin da mugun ruhu ya fita daga mutum, sai ya bi ta wuraren da ba mutane, yana neman hutu, amma ya kāsa samu, sai ya ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’
25 І прийшовши знайде її виметену й прибрану.
Sa’ad da ya koma, ya tarar da gidan a share da tsabta, kuma a shirye.
26 Тоді йде та бере сім инших духів, злїщих над себе; і, ввійшовши, домують там; і буде останнє чоловіка того гірше першого.
Sai ya je ya ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, sai su shiga su zauna a wurin. Ƙarshen wannan mutum kuwa zai fi farkonsa muni.”
27 Стало ся ж, як промовляв Він се, піднявши одна жінка зміж народу голос, каже Йому: Блаженна утроба, що носила Тебе, й соски, що ссав єси.
Da Yesu yake cikin faɗin waɗannan abubuwa, sai wata mace daga cikin taron ta ɗaga murya ta ce masa, “Mai albarka ce uwar da ta haife ka, wadda ka sha mamanta.”
28 Він же рече: Блаженні ж і ті, що слухають слово Боже, та й хоронять його.
Yesu ya amsa ya ce, “A maimakon, masu albarka ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma biyayya da ita.”
29 Як же народ громадив ся, почав глаголати: Кодло се лукаве; воно ознаки шукає, і не дасть ся ознака йому, тільки ознака Йони пророка.
Da taron mutane suka ƙaru, sai Yesu ya ce, “Wannan mugun zamani ne. Tana neman wani abin banmamaki, amma ba ko ɗaya da za a ba ta, sai dai ta Yunana.
30 Бо, як Йона був ознакою Ниневянам, так буде й Син чоловічий кодлу сьому:
Kamar yadda Yunana ya zama alama ga mutanen Ninebe, haka ma Ɗan Mutum zai zama ga zamanin nan.
31 Цариця полуденна встане на суд із чоловіками кодла сього, та й осудить їх: бо прийшла вона з краю землі послухати премудростї Соломонової; а ось більший Соломона тут,
A ranar shari’a, Sarauniyar Kudu za tă tashi tsaye tare da wannan zamani, ta yanke wa wannan zamani hukunci, domin ta zo daga ƙarshen duniya ta saurari hikimar Solomon, ga shi kuwa, shi wanda ya fi Solomon girma, na nan.
32 Ниневяне встануть на суд із кодлом сим, та й осудять його; бо покаялись по проповіді Йониній; а ось більший Йони тут.
A ranar shari’a, mutanen Ninebe za su tashi tsaye tare da wannan zamani, su yanke wa wannan zamani hukunci. Gama sun tuba sa’ad da Yunana ya yi musu wa’azi. Ga shi yanzu, shi wanda ya fi Yunana girma, na nan.
33 Ніхто ж, засьвітивши сьвічку, на потайному не ставить, нї під посудину, а на сьвічнику, щоб хто входить, сьвітло бачив.
“Babu wanda yakan ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta, ko ya rufe ta da murfi ba. A maimako, yakan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, don masu shiga su ga haske.
34 Сьвітло тїлу око; коли ж оце тїіо твоє ясне буде, то й все тїло твоє сьвітле: коли ж лихе буде, то й тїло твоє темне.
Idonka shi ne fitilar jikinka. Sa’ad da idanunka suna da lafiya, dukan jikinka ma na cike da haske, amma sa’ad da idanunka suna da lahani, dukan jikinka ma na cike da duhu.
35 Гледи ж оце, щоб сьвітло, що в тобі, не була темрява.
Ka lura fa, kada hasken da yake cikinka ya zamana duhu ne.
36 Коли ж тїло твоє все сьвітле, не маючи ніякої частини темної, то буде сьвітле все, як би сьвічка сяєвом просьвічувала тебе.
Saboda haka, in dukan jikinka yana cike da haske, ba inda ke da duhu, jikinka kuwa zai kasance da haske gaba ɗaya, kamar yadda hasken fitila yake haskaka ka.”
37 Як же Він промовляв, просив Його Фарисей один, щоб обідав у него; ввійшовши ж, сів за столом.
Da Yesu ya gama magana, sai wani Bafarisiye ya gayyace shi cin abinci tare da shi. Sai kuwa ya shiga ya zauna a tebur.
38 Фарисей же, побачивши, здивував ся, що перше не обмив ся перед обідом.
Amma Bafarisiyen ya lura cewa, Yesu bai wanke hannu kafin ya ci abinci ba, sai mamaki ya kama shi.
39 Рече ж Господь до него: Тепер ви, Фарисеї, верх чаші і блюда очищаєте; середина ж ваша повна здирства та лукавства.
Sai Ubangiji ya ce masa, “Ku Farisiyawa, kukan wanke bayan kwano da kwaf, amma a ciki kuna cike da kwaɗayi da mugunta.
40 Безумні! хиба, хто зробив верх, і середини не зробив.
Ku wawayen mutane! Ashe, wanda ya yi bayan, ba shi ne kuma ya yi cikin ba?
41 Тільки давайте милостиню з того, що є, і ось усе чисте вам буде.
Ku ba matalauta abin da yake cikin kwano, kuma kome zai zama muku da tsabta.
42 Та горе вам, Фарисеї! бо даєте десятину з мяти, рути і всякого зїлля, а минаєте суд і любов Божу. Се повинні були чинити, та й того не залишати.
“Kaitonku, Farisiyawa, domin kuna ba wa Allah zakka na na’ana’arku, da ƙarƙashinku, da kuma sauran ganyen lambunku iri-iri, amma kun ƙyale adalci da ƙaunar Allah. Ya kamata da kun kiyaye na ƙarshen, ban ba barin na farkon.
43 Горе вам, Фарисеї! бо любите перві сїдалища по школах і витання на торгах.
“Kaitonku, Farisiyawa, domin kun cika son wuraren zama masu daraja a majami’u, da kuma yawan gaisuwa a wuraren kasuwanci.
44 Горе вам, письменники та Фарисеї, лицеміри! бо ви мов гроби, що їх невидко, й люде, ходячи поверх них, не знають.
“Kaitonku, domin ku kamar kaburbura ne da ba a sa musu alama ba, waɗanda mutane suke takawa don rashin sani.”
45 Озвав ся ж один з законників, і каже Йому: Учителю, так говорячи, ти й вас обижаєш.
Sai ɗaya daga cikin masanan dokoki ya ce wa Yesu, “Malam, in ka faɗi waɗannan abubuwa haka, kai kuma ka zage mu ke nan.”
46 Він же рече: І вам, законникам, горе! що накдадуете людям тягарі котрі важко носити, а самі одним пальцем вашим не приторкнетесь до тягарів.
Yesu ya amsa ya ce, “Ku masanan dokoki ma, kaitonku, domin kun ɗora wa mutane kaya masu nauyi waɗanda da ƙyar suke ɗaukawa, amma ku da kanku ba za ku sa ko yatsa ɗaya, don ku taimake su ba.
47 Горе вам! що будуєте гроби пророкам, батьки ж ваші повбивали їх.
“Kaitonku, domin kun gina kaburbura saboda annabawa, nan kuwa kakannin-kakanninku ne suka kashe su.
48 Правдиво ви сьвідкуєте, і любі вам учинки батьків ваших; бо се вони повбивали їх, ви ж будуєте їм гроби.
Wannan ya shaida cewa kun amince da abin da kakannin-kakanninku suka yi. Sun karkashe annabawa, ku kuma kun gina kaburburansu.
49 Тим і премудрість Божа глаголе: Пішлю до них пророків та апостолів, і инших з них вони вбивати муть та гонити муть,
Saboda haka, Allah a cikin hikimarsa ya ce, ‘Zan aika musu da annabawa da manzanni. Za su kashe waɗansu, su kuma tsananta wa waɗansu.’
50 щоб відомстити за кров усїх пророків, пролиту від основання сьвіта кодлу сьому,
Saboda haka, alhakin jinin dukan annabawa da aka kashe, tun farkon duniya, yana kan wannan zamani,
51 від крові Авєля аж до крові Захарії, що поліг між жертївнею й храмом. Так, глаголю вам, відомстить ся, кодлу сьому.
wato, tun daga jinin Habila, har zuwa jinin Zakariya, wanda aka kashe tsakanin bagade da mazauni. I, ina gaya muku, alhakinsu duka yana kan wannan zamani.
52 Горе вам, законники! що ви взяли ключ розуміння: самі не ввійшли, й тим, що входять, заборонили.
“Kaitonku, masanan dokoki, domin kun ɗauke mabuɗin ilimi. Ku kanku ba ku shiga ba, kuma kun hana wa waɗanda suke shiga, su shiga.”
53 Як же промовляв Він се до них, стали письменники та Фарисеї вельми наступати на Него, й допитуватись у Него про многі речі,
Da Yesu ya bar wurin, sai Farisiyawa da malaman dokoki suka fara gaba mai tsanani da shi, kuma suna tsokanansa da tambayoyi.
54 чигаючи на Него й шукаючи вхопити що з уст Його, щоб обвинувати Його.
Suna fakonsa, don su kama shi a kan wata magana da zai faɗa.