< Від Івана 1 >

1 Упочинї було Слово, й Слово було в Бога, й Бог було Слово.
A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
2 Воно було в починї у Бога.
Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
3 Все Ним стало ся; і без Него не стало ся нїщо, що стало ся.
Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
4 У Йому життє було: й життв було сьвітлом людям.
A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
5 І сьвітло у темряві сьвітить, і темрява Його не обняла.
Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
6 Був чоловік посланий від Бога, ймя йому Йоан.
Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
7 Сей прийшов на сьвідкуваннє, щоб сьвідкувати про сьвітло, щоб усї вірували через него.
Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
8 Не був він сьвітло, а щоб сьвідкувати про сьвітло.
Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
9 Було сьвітло правдиве, що просьвічує кожного чоловіка, що приходить на сьвіт.
Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
10 На сьвітї був, і сьвіт Ним настав, і сьвіт Його не пізнав.
Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
11 У своє прийшов, і свої не прийняли Його.
Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
12 Которі ж прийняли Його, дав їм власть дїтьми Божими стати ся, що вірують в імя Його:
Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
13 що не від крові, нї від хотіння тілесного, нї від хотїння мужеського, а від Бога родили ся.
Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
14 І Слово тїлом стало ся, і пробувало між нами (й бачили ми славу Його, славу, яко Єдинородного від Отця), повне благодати і правди.
Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
15 Йоан сьвідкує про Него, й покликував, глаголючи: Се той, про кого казав я: За мною грядущий поперед мене був; бо перш мене був.
Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
16 І з повноти Його ми всї прийняли й благодать за благодать.
Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
17 Бо закон через Мойсея даний був; благодать і правда через Ісуса Христа стала ся.
Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
18 Бога ніхто не бачив ніколи; единородний Син, що в лонї Отця, той вияснив.
Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
19 І се сьвідченнє Йоанове, як післали Жиди з Єрусалиму священиків та левитів, щоб спитали Його: Хто ти єси?
Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
20 І визнав, і не відпер ся; а визвав: Що я не Христос.
Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
21 І питали його: Що ж? Ілия єси ти? І рече: Нї. Пророк єси ти? І відказав: Нї.
Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
22 Казали ж йому: Хто ж єси? щоб нам одповідь дати тим, що післали нас. Що кажеш про себе?
Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
23 Рече: Я голос покликуючого в пустинї: Випростайте дорогу Господню, як глаголав Ісаїя пророк.
Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
24 А послані були з Фарисеїв.
Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
25 І питали вони його, й казали йому: Чого ж хрестиш, коли ти не Христос, нї їлия, нї пророк.
“To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
26 Відказав їм Йоан, глаголючи: Я хрещу вас водою; серед вас же стоїть, котрого ви не знаєте:
Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
27 се за мною Грядущий, що поперед мене був; котрому я недостоєя розвязати ременя обувя Його.
shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
28 Се в Витаварі стало ся, за Йорданом, де Йоан хрестив.
Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
29 Назавтра бачить Йоан, що Ісус ійде до него, й рече: Ось Агнець Божий, що бере на себе гріх сьвіта.
Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
30 Ое Той, про кого я казав: За мною гряде муж, що поперед мене був, бо перше мене був.
Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
31 І я не знав Його, та, щоб явив ся Ізраїлеві, для того прийшов я, хрестячи водою.
Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
32 І сьвідкував Йоан, глаголючи: Що бачив я Духа, злинувшого як голуб з неба, і став він над Ним.
Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
33 І я не знав Його; та пославший мене хрестити водою, той менї глаголав: На кого побачиш, що Дух злине та стане над Ним, се той, що хрестить Духом сьвятим.
Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
34 І бачив я, і сьвідкував, що се є Син Божий.
Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
35 Назавтра знов стояв Йоан і два з учеників його;
Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
36 і, споглянувши на Ісуса йдучого, рече: ось Агнець Божий.
suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
37 І чули його два ученики глаголючого, й пійшли слїдом за Ісусом.
Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
38 І обернувшись Ісус та побачивши їх слїдом ідучих, рече їм: Чого шукаєте? Вони ж сказали Йому: Рави (що єсть перекладом: Учителю), де пробуваєш?
Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
39 Рече їм: Ідїть і подивіть ся. Пійшли вони, та й бачили, де пробуває, і перебули в Него день той; було ж коло десятої години.
Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
40 Один з двох, що чули від Йоана та й пійшли слїдом за ним, був Андрей, брат Симона Петра.
Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
41 Він знаходить первий брата свого Симона, й каже йому: Знайшли ми Месию (що єсть перекладом: Христос).
Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
42 І привів його до Ісуса. Поглянувши ж на него Ісус, рече: Ти єси Симон, син Йони; ти назвеш ся Кифа (що єсть перекладом: Петр).
Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
43 Назавтра хотів Ісус вийти в Галилею і знаходить Филипа, й рече йому: Йди слїдом за мною.
Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
44 Був же Филип із Витсаїди, з города Андреєвого та Петрового.
Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
45 Знаходить Филип Натанаїла, й каже йому: Про кого писав Мойсей у законї й пророки, знайшли ми, Ісуса, сина Йосифового, що з Назарету.
Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
46 І каже Натанаїл до него: З Назарету хиба може що добре бути? Каже йому Филип: Іди та й подивись!
Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
47 Побачив Ісус Натанаїла, йдучого до Него, й рече про него: Ось справді Ізраїлитянин, що в йому підступу нема.
Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
48 Каже Йому Натанаїл: Звідкіля мене знаєш? Озвавсь Ісус і рече йому: Перш нїж Филип покликав тебе, як був єси під смоківницею, бачив я тебе.
Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
49 Озвавсь Натанаїл і каже Йому: Рави, Ти єси Син Божий, Ти єси цар Ізраїлїв.
Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
50 Озвавсь Ісус і рече йому: Що сказав тобі: Я бачив тебе під смоківницею, то й віруєш? Більше сього бачити меш.
Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
51 І рече йому: Істино, істино глаголю вам: Від нині бачити мете небо відкрите, й ангелів Божих, що сходять угору і вниз на Сина чоловічого.
Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”

< Від Івана 1 >