< Дії 12 >

1 Під той же час здвигнув цар Ірод руки, щоб мучити деяких із церкви.
Kusan a wannan lokaci ne Sarki Hiridus ya kama waɗansu da suke na ikkilisiya, da niyya ya tsananta musu.
2 Вбив же Якова, брата Йоанового, мечем,
Ya sa aka kashe Yaƙub, ɗan’uwan Yohanna, da takobi.
3 а видївши, що се подобаєть ся Жидам, постановив схопити й Петра. (Були ж дні опрісноків.)
Sa’ad da ya ga wannan ya faranta wa Yahudawa rai, sai ya kama Bitrus shi ma. Wannan ya faru kwanakin Bikin Burodi Marar Yisti.
4 І схопивши його, посадив у темницю, передавши чотиром четверицям воїнів стерегти його, задумавши після пасхи вивести його перед народ.
Bayan ya kama shi, sai ya sa shi a kurkuku, ya danƙa shi a hannun soja hurhuɗu kashi huɗu, don su yi gadinsa. Hiridus ya yi niyyar ya yi masa shari’a a gaban mutane bayan Bikin Ƙetarewa.
5 Стережено ж Петра в темниці; церква ж без перестану молилась Богу за него.
Saboda haka aka tsare Bitrus a kurkuku, amma ikkilisiya ta nace da addu’a ga Allah dominsa.
6 Як же мав його вивести Ірод, спав тієї ночи Петр між двома воїнами, скований двома залїзами; а сторожі перед дверима стерегли темниці.
A daren da in gari ya waye da Hiridus yake niyyar kawo shi domin a yi masa shari’a, Bitrus yana barci tsakanin sojoji biyu, daure da sarƙoƙi biyu, masu gadi kuma suna bakin ƙofa.
7 І ось ангел Господень став перед ним, і сьвітло засияло в будинку; торкнувши ж у бік Петра, підвів його, говорячи: Уставай боржій. І поспадали кайдани з рук його.
Ba zato ba tsammani sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana haske kuma ya haskaka a ɗakin. Ya bugi Bitrus a gefe ya kuma tashe shi ya ce, “Maza, ka tashi!” Sarƙoƙin kuwa suka zube daga hannuwansa.
8 І рече ангел до него: Підпережись та підвяжи постоли твої. Зробив же так. І рече йому: Надїнь одежу твою, та йди за мною.
Sa’an nan mala’ikan ya ce masa, “Ka sa rigunarka da takalmanka.” Bitrus kuwa ya sa. Mala’ikan ya faɗa masa cewa, “Ka yafa mayafinka ka bi ni.”
9 І, вийшовши, вийшов слїдом за ним, і не знав, що се правда, що сталось через ангела; думав же, що видїннє бачить.
Bitrus ya bi shi suka fita kurkukun, amma bai ma san cewa abin da mala’ikan yake yi tabbatacce ne ba; yana tsammani wahayi yake gani.
10 Минувши ж перву сторожу й другу, прийшли до залїзних воріт, що вели в город, котрі самі собою відчинились їм; і вийшовши пройшли одну улицю, і зараз відступив ангел від него.
Suka wuce masu gadi na fari da na biyu, suka kuma isa ƙofar ƙarfe ta shiga birni. Ƙofar kuwa ta buɗe musu da kanta, suka kuma wuce. Sa’ad da suka yi tafiya tsawon wani titi, nan take mala’ikan ya bar shi.
11 І, прийшовши Петр до себе, рече: Тепер знаю справді, що післав Господь ангела свого, і вирвав мене з руки Іродової і від усього дожидання народу Жидівського.
Sai Bitrus ya dawo hankalinsa ya ce, “Yanzu na sani ba shakka Ubangiji ne ya aiki mala’ikansa yă cece ni daga hannun Hiridus da kuma dukan mugun fatan Yahudawa.”
12 І зміркувавши, прийшов до хати Мариї, матери Йоана, званого Марком, де многі зібрались і молились.
Da ya gane haka, sai ya tafi gidan Maryamu uwar Yohanna, wanda ake kuma kira Markus, inda mutane da yawa suka taru suna addu’a.
13 Як же постукав Петр у сїнешні двері, вийшла послухати дївчина, на ймя Рода;
Bitrus ya ƙwanƙwasa ƙofar waje, sai wata mai aiki a gidan da ake kira Roda ta zo tă ji ko wane ne.
14 і, пізнавши голос Петра, з радощів не відчинила дверей, а вбігши, сповістила, що Петр стоїть під дверима.
Da ta gane muryar Bitrus, ta cika da murna ta gudu ta koma ba tare da ta buɗe ƙofar ba, sai ta koma a guje ta ce da ƙarfi, “Ga Bitrus a bakin ƙofa!”
15 Вони ж сказали до неї: Збожеволіла єси. Вона ж таки говорила, що се так. Вони ж казали: Се ангел його.
Sai suka ce mata, “Kina hauka.” Da ta nace cewa shi ne, sai suka ce, “To, lalle, mala’ikansa ne.”
16 Петр же не перестав стукати; відчинивши ж, увиділи його, та й здивувались.
Amma Bitrus ya yi ta ƙwanƙwasawa. Da suka buɗe ƙofar suka kuma gan shi, sai suka yi mamaki.
17 Махнувши ж їм рукою, щоб мовчали, оповів їм, як Господь вивів його з темниці. Рече ж: Сповістіть Якова та братів про се. І, вийшовши, пійшов у друге місце.
Bitrus ya yi musu alama da hannunsa su yi shiru sai ya bayyana yadda Ubangiji ya fitar da shi daga kurkuku. Ya ce, “Ku gaya wa Yaƙub da kuma’yan’uwa game da wannan,” sa’an nan ya tashi ya tafi wani wuri.
18 Скоро ж настав день, зробивсь немалий переполох між воїнами, що стало ся з Петром.
Da safe, hargitsin da ya tashi tsakanin sojojin ba ƙarami ba ne, a kan abin da ya sami Bitrus.
19 Ірод же, пошукавши його, й не знайшовши, судив сторожів, та й звелїв покарати їх. І перейшовши з Юдеї в Кесарию, жив (там).
Bayan Hiridus ya neme shi bai same shi ba, sai ya tuhumi masu gadin, ya kuma ba da umarni a kashe su. Sa’an nan Hiridus ya tashi daga Yahudiya ya tafi Kaisariya ya kuma yi’yan kwanaki a can.
20 Лютував же Ірод на Тирян та на Сидонян. Прийшовши ж однодушно до него, й приєднавши Бласта, царського постельника, просили примирря; бо земля їх живилась од царської.
Yana da rashin jituwa da mutanen Taya da na Sidon; sai suka haɗa kai suka nemi ganawa da shi. Bayan suka sami goyon bayan Bilastus, amintaccen bawan sarki, sai suka nemi salama, domin sun dogara ga ƙasar sarkin don samun abincinsu.
21 Призначеного ж дня Ірод, одігшись у царські шати і сівши на престолі, промовляв до них:
A ranar da aka shirya Hiridus, sanye da kayan sarautarsa, ya zauna a gadon sarautarsa ya kuma ya wa mutanen jawabi.
22 Народ же покликував: Голос Бога, а не чоловіка!
Suka tā da murya suka ce, “Wannan muryar wani allah ne, ba ta mutum ba.”
23 Зараз же поразив його ангел Господень за те, що не віддав слави Богу; і з'їли його черви, і вмер.
Nan take, domin Hiridus bai yi wa Allah yabo ba, wani mala’ikan Ubangiji ya buge shi, tsutsotsi kuwa suka cinye shi ya kuma mutu.
24 Слово ж Боже росло і множилось.
Amma maganar Allah ta ci gaba da ƙaruwa ta kuma bazu.
25 Варнава ж та Савло вернулись із Єрусалиму, сповнивши службу, і взявши з собою Йоана, званого Марком.
Sa’ad da Barnabas da Shawulu suka kammala aikinsu, sai suka komo daga Urushalima, tare da Yohanna, wanda ake kira Markus.

< Дії 12 >