< Від Матвія 12 >
1 У той час Ісус проходив у Суботу через засіяні поля пшениці. Його учні зголодніли й почали зривати колосся та їсти.
A wannan lokaci, Yesu ya tafi a ranar Asabaci, ya bi cikin gonar hatsi. Almajiransa na jin yunwa, sai suka fara zagar hatsi suna ci.
2 Фарисеї ж, побачивши це, сказали Йому: ―Ось Твої учні роблять те, чого не дозволено робити в Суботу!
Amma da Farisawa suka gan su, sai su ka ce wa Yesu. “Duba, almajiranka su na yin abin da doka ta haramta a ranar Asabaci.”
3 Тоді Він сказав їм: ―Ви не читали, що зробив Давид, коли зголоднів він, а також і ті, що були з ним?
Amma Yesu ya ce masu, “Baku karanta abin da Dauda ya yi ba, lokacin da ya ke jin yunwa, tare da mazan da ke tare da shi?
4 Як увійшов у Дім Божий та з’їв хліби покладання, котрі не дозволено було їсти ані йому, ані тим, хто був із ним, а тільки священникам?
Yadda ya shiga gidan Allah, ya ci gurasar alfarwa da doka ta hana shi ko mazan da ke tare da shi su ci, sai dai Firistoci ne kawai doka ta basu damar ci?
5 Або хіба ви не читали в Законі, що в Суботу в Храмі священники порушують Суботу й залишаються невинними?
Sa'annan ba ku karanta cikin shari'a cewa, a ranar Asabaci, Firistoci da ke cikin haikali na sabawa ranar Asabaci, amma kamar ba su yi laifi ba?
6 Але Я кажу вам: тут щось більше, ніж Храм.
Amma ina tabbatar maku da cewa, wani wanda ya fi haikali girma yana nan.
7 Якби ви зрозуміли, що означає: «Милосердя хочу, а не жертви», то не засуджували б невинних.
In da kun san ma'anar wannan 'Na fi son jinkai fiye da hadaya,' da baku shari'anta wa marar laifi ba.
8 Бо Син Людський – Господь Суботи.
Gama Dan mutum shine Ubangijin Asabaci.”
9 Вирушивши далі, Він зайшов у їхню синагогу.
Sa'annan Yesu ya bar wannan wuri, ya shiga majami'ar su.
10 Там був чоловік із всохлою рукою. І щоб звинуватити Його, вони запитали: ―Чи дозволено зцілювати в Суботу?
Sai ga wani mutum wanda hannun sa ya shanye, sai Farisawa suka tambayi Yesu, cewa, “Doka ta halarta a yi warkarwa a ranar Asabaci?” Domin su zarge shi a kan zunubi.
11 Він же промовив: ―Хто з вас, маючи одну вівцю, якщо вона впаде в Суботу в яму, не візьме й не витягне її?
Yesu ya ce masu, “Wanene a cikin ku, wanda idan ya na da tunkiya guda, sa'annan tunkiyar nan ta fada a rami mai zurfi a ranar Asabaci ba zai kamo ta ya fitar da ita ba?
12 Наскільки ж людина цінніша за вівцю! Тому в Суботу дозволено робити добро.
Yaya za a kwatanta darajar mutum da tunkiya! Saboda haka ya halarta a yi alheri ranar Asabaci.”
13 Тоді сказав чоловікові: ―Простягни свою руку! Той простягнув, і його рука стала здоровою, як і друга.
Sai Yesu ya ce wa mutumin nan “Mika hannun ka.” Ya mike hannunsa, sai hannun nan ya dawo lafiyaye kamar dayan hannunsa.
14 Фарисеї ж вийшли та радились проти Нього, як Його вбити.
Amma Farisawa su ka fita waje su ka fara mugun shiri domin sa. Su na neman hanyar da za su kashe shi.
15 Дізнавшись [про це], Ісус пішов звідти. За Ним пішло багато людей, і Він зцілив їх усіх.
Da Yesu ya fahimci wannan, sai ya janye kan sa daga nan. Mutane da dama su ka bi shi, ya warkar da su duka.
16 Однак наказав їм, щоб не виявляли Його,
Ya dokace su da kada su bayyana shi ga kowa,
17 аби збулося сказане через пророка Ісаю:
domin ya zama gaskiyar abin da aka fada ta wurin annabi Ishaya, cewa,
18 «Ось Слуга Мій, Якого Я обрав, Мій Улюблений, Якого вподобала душа Моя. Я покладу Духа Мого на Нього, і Він звіщатиме суд народам.
“Dubi, bawa na zababbe; kaunatacce na, wanda ya ke faranta mani raina sosai. Zan sa Ruhu na bisan sa, za ya furta hukunci zuwa al'ummai.
19 Він не буде ні сперечатися, ні кричати, і ніхто не почує Його голосу на вулицях.
Ba za ya yi jayayya ko tada murya ba, babu wanda za ya ji muryar sa a karabku.
20 Надломленої тростини Він не доламає, ґнота світильника, що тліє, не загасить, доки не встановить правосуддя.
Ba zai karya kara da ya tankwashe ba; ba zai kashe fitilar da ta kusa mutuwa ba; sai ya kawo hukunci ga nasara.
21 І на Його ім’я покладатимуть надію народи».
Sa'annan al'ummai za su dogara a ga sunansa.
22 Тоді привели до Нього біснуватого – сліпого та німого. [Ісус] зцілив його, так що німий говорив та бачив.
Sa'annan wani mutum, makaho ne, kurma kuma, aljannu kuma na cikinsa, an kawo shi wurin Yesu. Ya warkar da shi, ya sami ganin gari ya kuma yi magana.
23 Усі люди дивувались та говорили: ―Чи це не Син Давидів?
Jama'a su ka yi mamaki kwarai, su na cewa, “Ko wannan ne Dan Dawuda?”
24 Але фарисеї, почувши [це], казали: ―Він виганяє демонів не інакше, як [силою] Вельзевула, володаря демонів.
Amma da Farisawa su ka ji wannan al'ajibi, sai su ka ce, “Mutumin nan yana fitar da aljannu ta wurin Bahalzabuba sarkin aljannu ne.”
25 [Ісус] же, знаючи їхні думки, відповів: ―Кожне царство, розділене в собі, буде спустошене, і кожне місто чи дім, розділені в собі, не встоять.
Amma Yesu ya san tunanin su, sai ya ce. “Duk mulkin da ya rabu gaba da kan sa, ba zaya tsaya ba, duk wani birni da ya rabu ba zai tsaya ba, ko gida da ya tsage, za ya rushe.
26 Якщо сатана виганяє сатану, то він розділився в собі самому. Як же тоді встоїть його царство?
Idan Shaidan ya fitar da Shaidan, ya rabu gaba da kansa. Yaya mulkin sa za ya tsaya?
27 І якщо Я виганяю демонів Вельзевулом, то ким виганяють ваші сини? Тому вони будуть вашими суддями.
Idan Ina fitar da aljannu da ikon Ba'alzabuba, ta wurin wa masu bin ku su ke fitar da su? Saboda haka, su za su shari'anta ku.
28 Але якщо Я Духом Божим виганяю демонів, то прийшло до вас Царство Боже.
Amma idan ina fitar da aljannu da Ruhun Allah ne, hakika mulkin Allah ya zo gare ku.
29 Або як може хтось увійти в дім сильного та забрати його майно, якщо спочатку не зв’яже сильного? Лише тоді пограбує його дім.
Kuma ta yaya mutum za ya shiga gidan mai karfi ya kwashe masa kaya ba tare da ya fara daure shi ba? Sa'annan ne za ya iya satar masa kaya daga gidansa.
30 Хто не зі Мною, той проти Мене; і хто не збирає зі Мною, той розкидає.
Wanda baya tare da ni yana gaba da ni ke nan, wanda kuma baya tarawa tare da ni, yana watsarwa ne.
31 Тому кажу вам: усякий гріх та богохульство проститься людям, але богохульство проти Духа не проститься.
Saboda haka ina ce maku, kowanne zunubi da sabo, za a gafarta wa mutum, amma sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta shi ba.
32 І якщо хтось скаже слово проти Сина Людського, йому проститься, але якщо хтось скаже проти Святого Духа, не проститься йому ні в цьому віці, ні в майбутньому. (aiōn )
Duk wanda yayi batanci ga Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma duk wanda yayi batanci game da Ruhu Mai Tsarki ba za a gafarta masa ba, a nan duniya da har abada. (aiōn )
33 Або визнайте дерево добрим і плід його добрим, або визнайте дерево поганим і плід його поганим. Бо дерево пізнається за плодом.
Ko dai a mai da itace mai kyau 'ya'yansa kuma su yi kyau, ko a mai da itace marar kyau 'ya'yansa kuma marasa kyau, gama ana sanin itace ta wurin 'ya'yansa.
34 Роде гадючий, як ви можете казати добре, будучи злими? Адже чим переповнене серце, те говорять вуста.
Ku 'ya'yan macizai, tun da ku miyagu ne, yaya za ku iya fadin abubuwa nagari? Gama daga cikar zuciya baki ke magana.
35 Добра людина з доброї скарбниці виносить добро, а погана людина з лихого скарбу виносить зло.
Mutumin kirki daga ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwa masu kyau, mugun mutum kuma daga mummunar ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwan mugunta.
36 Кажу вам: за кожне пусте слово, яке скажуть люди, вони відповідатимуть у день суду.
Sa'annan ina ce maku a ranar shari'a, mutane za su bada lissafin abubuwan banza da su ka fadi.
37 Бо з твоїх слів будеш виправданий і з твоїх слів будеш засуджений.
Gama ta wurin maganganun ku, za a 'yantar da ku, ta wurin maganganun ku kuma za a kashe ku.”
38 Тоді деякі книжники та фарисеї промовили: ―Учителю, ми хочемо побачити якесь знамення від Тебе.
Sa'annan wadansu Malaman Attaura, da Farisawa suka amsa suka ce wa Yesu, “Mallam, muna so mu ga wata alama daga gare ka.”
39 [Ісус] у відповідь промовив: ―Рід лукавий та невірний шукає знамення, та не дасться йому знамення, хіба що тільки знамення пророка Йони.
Amma Yesu ya amsa ya ce masu, “Mugun zamani da mazinaciyar tsara, su na bukutar alama. Amma babu alamar da za a ba su, sai dai alamar annabi Yunusa.
40 Адже так, як Йонабув у череві кита три дні та три ночі, так буде й Син Людський у серці землі три дні та три ночі.
Gama yadda Yunusa ya yi kwana uku da dare uku a cikin babban kifi, haka ma Dan Mutum zaya yi kwana uku da dare uku a cikin zuciyar kasa.
41 Люди Ніневіївстануть на суд із цим родом і засудять його, бо вони покаялись через проповідь Йони, а ось тут Хтось більший за Йону.
Mutanen Nineba za su tsaya a ranar shari'a da wannan zamani sannan su kashe su. Domin sun tuba da suka ji wa'azin Yunusa, amma duba wanda ya fi Yunusa yana nan.
42 Цариця Півднявстане на суд із цим родом і засудить його, бо вона прийшла з далекого краю землі послухати Соломонову мудрість, а ось тут Хтось більший за Соломона.
Sarauniyar Kudu za ta tashi da mutanen wannan zamani ta kuma kashe su. Ta zo daga karshen duniya domin ta ji hikimar Sulaimanu, kuma duba, wanda ya fi Sulaimanu yana nan.
43 Коли нечистий дух виходить із людини, то йде в місця безводні шукати відпочинку й, не знаходячи,
Idan kazamin ruhu ya rabu da mutum, ya kan wuce ya nemi wuraren da ruwa yake domin ya huta, amma bai samu ba.
44 каже: «Повернусь я у дім свій, звідки вийшов». І, повернувшись, знаходить його порожнім, заметеним та прибраним.
Sai ya ce, 'zan koma gidana inda na fito'. Bayan ya dawo, sai ya tarar da gidan nan an share shi ya zama da tsabta.
45 Тоді він іде й бере з собою інших сімох духів, гірших за себе, і входять та живуть там. І для людини останнє стає гіршим за попереднє. Так буде і з цим злим родом.
Sai ya koma ya kawo wadansu ruhohi guda bakwai, wadanda su ka fi shi mugunta, sa'annan dukan su su zo su zauna a nan. Sa'annan yanayin mutumin nan na karshe ya fi na farko muni. Haka zaya kasance ga wannan mugun zamani.
46 Коли [Ісус] ще говорив до народу, прийшли Його мати та брати і, стоячи надворі, бажали говорити з Ним.
Sa'adda Yesu ya ke yi wa Jama'a jawabi, sai mahaifiyarsa da 'yan'uwansa su ka zo su ka tsaya a waje, suna neman su yi magana da shi.
47 Хтось сказав Йому: ―Ось Твоя мати й Твої брати стоять надворі, бажаючи говорити з Тобою.
Sai wani ya ce masa, “Duba, mahaifiyarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai”.
48 Він же у відповідь сказав тому, хто говорив: ―Хто Моя мати і хто Мої брати?
Amma Yesu ya amsa ya ce wa shi wanda ya gaya masa, “Wacece mahaifiyata? Kuma su wanene 'yan'uwana?”
49 І, показавши рукою на Своїх учнів, промовив: ―Ось Моя мати та Мої брати.
Sai ya mika hannu ya nuna almajiransa ya ce, “Duba, ga mahaifiyata da 'yan'uwana!
50 Бо той, хто виконує волю Мого Небесного Отця, є Моїм братом, сестрою і матір’ю.
Gama duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda ya ke cikin sama, shine dan'uwana, da 'yar'uwata da mahaifiyata.”