< Zekeriya 1 >
1 Darius'un krallığının ikinci yılının sekizinci ayında RAB İddo oğlu Berekya oğlu Peygamber Zekeriya aracılığıyla şöyle seslendi:
A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
2 “RAB atalarınıza çok öfkelendi.
“Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
3 Bu nedenle halka de ki, Her Şeye Egemen RAB böyle diyor: ‘Her Şeye Egemen RAB, bana dönün’ diyor; ‘Ben de size dönerim diyor Her Şeye Egemen RAB.
Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 Atalarınız gibi davranmayın! Önceki peygamberler, Her Şeye Egemen RAB kötü yollarınızdan ve kötü uygulamalarınızdan dönün diyor, diyerek onları uyardılar. Ne var ki, onlar dinlemediler, bana aldırış etmediler. Böyle diyor RAB.
Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
5 Hani atalarınız nerede? Peygamberler de sonsuza kadar mı yaşar?
Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
6 Peygamber kullarıma buyurduğum sözler ve kurallar atalarınıza ulaşmadı mı?’ “Onlar da dönüp, ‘Her Şeye Egemen RAB yollarımıza ve uygulamalarımıza bakarak bizim için ne düşündüyse aynen yaptı’ dediler.”
Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
7 Darius'un krallığının ikinci yılında, on birinci ay olan Şevat ayının yirmi dördüncü günü RAB İddo oğlu Berekya oğlu Peygamber Zekeriya'ya görümlerle seslendi.
A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
8 Gece vadideki mersin ağaçlarının arasında kızıl ata binmiş bir adam gördüm. Arkasında kızıl, kula ve beyaz atlar vardı.
Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
9 “Efendim, bunlar ne?” diye sordum. Benimle konuşan melek, “Bunların ne olduğunu sana göstereceğim” diye yanıtladı.
Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
10 Mersin ağaçları arasında duran adam da, “Bunlar dünyayı dolaşmak için RAB'bin gönderdikleridir” diye açıkladı.
Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
11 Mersin ağaçları arasında duran RAB'bin meleğine, “Dünyayı dolaştık” dediler, “İşte bütün dünya esenlik ve güvenlik içinde!”
Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
12 Bunun üzerine RAB'bin meleği, “Ey Her Şeye Egemen RAB, yetmiş yıldır öfkelendiğin Yeruşalim'den ve Yahuda kentlerinden sevecenliğini ne zamana dek esirgeyeceksin?” dedi.
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
13 RAB benimle konuşan meleği tatlı, avutucu sözlerle yanıtladı.
Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
14 Bunun üzerine benimle konuşan melek, “Şunu duyur!” dedi, “Her Şeye Egemen RAB, ‘Yeruşalim ve Siyon için büyük kıskançlık duyuyorum’ diyor,
Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
15 ‘Tasasız uluslara ise çok öfkeliyim; çünkü ben biraz öfkelenmiştim, onlarsa kötülüğe kötülük kattılar.’
amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
16 “Onun için RAB, ‘Yeruşalim'e sevecenlikle döneceğim’ diyor, ‘Tapınağım orada yeniden kurulacak ve Yeruşalim üzerine ölçü ipi çekilecek!’ Böyle diyor Her Şeye Egemen RAB.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
17 “Şunu da duyur: Her Şeye Egemen RAB, ‘Kentlerim yine bollukla dolup taşacak’ diyor, ‘Ben RAB, Siyon'u yine avutacağım, Yeruşalim'i yine seçeceğim.’”
“Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
18 Sonra gözlerimi kaldırıp baktım, dört boynuz vardı.
Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
19 Benimle konuşan meleğe, “Bunlar ne?” diye sordum. Melek, “Bunlar Yahuda, İsrail ve Yeruşalim halkını dağıtmış olan boynuzlardır” diye karşılık verdi.
Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
20 Sonra RAB bana dört usta gösterdi.
Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
21 “Bunlar ne yapmaya geliyor?” diye sordum. Melek, “Şu boynuzlar Yahuda halkını öyle dağıttı ki, kimse başını kaldıramadı” dedi, “Bu ustalar da Yahuda halkını dağıtmak için boynuz kaldıran ulusları yıldırıp boynuzlarını yere çalmaya geldiler.”
Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”