< Vahiy 19 >
1 Bundan sonra gökte büyük bir kalabalığın sesini andıran yüksek bir ses işittim. “Haleluya!” diyorlardı. “Kurtarış, yücelik ve güç Tanrımız'a özgüdür.
Bayan wannan sai na ji abin da ya yi kamar ƙasaitaccen taron mutane a sama, suna cewa, “Halleluya! Ceto da ɗaukaka da iko sun tabbata ga Allahnmu,
2 Çünkü O'nun yargıları doğru ve adildir. Yeryüzünü fuhşuyla yozlaştıran Büyük fahişeyi yargılayıp Kendi kullarının kanının öcünü aldı.”
gama hukuncinsa daidai ne, mai adalci kuma. Ya hukunta babbar karuwan nan wadda ta ɓata duniya da zinace zinacenta. Ya rama jinin bayinsa a kanta.”
3 İkinci kez, “Haleluya! Onun dumanı sonsuzlara dek tütecek” dediler. (aiōn )
Suka sāke tā da murya suka ce, “Halleluya! Hayaƙin yake fitowa daga wurinta ya yi ta tashi sama har abada abadin.” (aiōn )
4 Yirmi dört ihtiyarla dört yaratık yere kapanıp, “Amin! Haleluya!” diyerek tahtta oturan Tanrı'ya tapındılar.
Dattawan nan ashirin da huɗu da halittu huɗun nan masu rai suka fāɗi suka yi wa Allah sujada, wannan da yake zaune a kursiyi. Suka tā da murya suka ce, “Amin, Halleluya!”
5 Sonra tahttan bir ses yükseldi: “Ey Tanrımız'ın bütün kulları! Küçük büyük, O'ndan korkan hepiniz, O'nu övün!”
Sa’an nan wata murya ta fito daga kursiyin, tana cewa, “Ku yabi Allahnmu, dukanku da kuke bayinsa, ku da kuke tsoronsa, babba da yaro!”
6 Ardından büyük bir kalabalığın, gürül gürül akan suların, güçlü gök gürlemelerinin sesine benzer sesler işittim. “Haleluya!” diyorlardı. “Çünkü Her Şeye Gücü Yeten Rab Tanrımız Egemenlik sürüyor.
Sai na ji wani abu mai ƙara kamar ƙasaitaccen taron mutane, kamar rurin ruwaye masu gudu da kuma kamar bugun tsawa mai ƙarfi, suna tā da murya suna cewa, “Halleluya! Gama Ubangiji Allahnmu Maɗaukaki ne yake mulki.
7 Sevinelim, coşalım! O'nu yüceltelim! Çünkü Kuzu'nun düğünü başlıyor, Gelini hazırlandı.
Bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna mu kuma ɗaukaka shi! Domin lokacin auren Ɗan Ragon ya yi, amaryarsa kuwa ta shirya kanta.
8 Giymesi için ona temiz ve parlak İnce keten giysiler verildi.” İnce keten kutsalların adil işlerini simgeler.
Aka ba ta lallausan lilin, mai haske da tsabta ta sanya.” (Lallausan lilin yana misalta ayyukan adalci na tsarkaka.)
9 Sonra melek bana, “Yaz!” dedi. “Ne mutlu Kuzu'nun düğün şölenine çağrılmış olanlara!” Ardından ekledi: “Bunlar gerçek sözlerdir, Tanrı'nın sözleridir.”
Sai mala’ikan ya ce mini, “Rubuta, ‘Masu albarka ne waɗanda aka gayyace su zuwa bikin auren Ɗan Ragon!’” Sai ya ƙara da cewa, “Waɗannan su ne kalmomin Allah da gaske.”
10 Ona tapınmak üzere ayaklarına kapandım. Ama o, “Sakın yapma!” dedi. “Ben de senin ve İsa'ya tanıklığını sürdüren kardeşlerin gibi bir Tanrı kuluyum. Tanrı'ya tap! Çünkü İsa'ya tanıklık, peygamberlik ruhunun özüdür.”
Da wannan sai na fāɗi a gabansa, don in yi masa sujada. Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni ma abokin bauta ne da kai da kuma’yan’uwanka waɗanda suke riƙe da shaidar Yesu. Ka yi wa Allah sujada! Domin shaidar Yesu ita ce ruhun annabci.”
11 Bundan sonra göğün açılmış olduğunu, beyaz bir atın orada durduğunu gördüm. Binicisinin adı Sadık ve Gerçek'tir. Adaletle yargılar, savaşır.
Sai na ga sama a buɗe can kuwa a gabana ga farin doki, sunan mahayinsa Mai Aminci da Mai Gaskiya ne. Da adalci yake shari’a yake kuma yaƙi.
12 Gözleri alev alev yanan ateş gibidir. Başında çok sayıda taç var. Üzerinde kendisinden başka kimsenin bilmediği bir ad yazılıdır.
Idanunsa sun yi kamar harshen wuta, a kansa kuwa akwai rawani masu yawa. Yana da suna rubuce a kansa da babu wanda ya sani sai dai shi.
13 Kana batırılmış bir kaftan giymişti. Tanrı'nın Sözü adıyla anılır.
Yana saye da rigar da aka tsoma a jini, sunansa kuwa Kalman Allah ne.
14 Beyaz, temiz, ince ketene bürünmüş olan gökteki ordular, beyaz atlara binmiş O'nu izliyorlardı.
Mayaƙan sama suna biye da shi, suna hawan fararen dawakai, saye da fararen tufafi masu tsabta na lallausan lilin.
15 Ağzından ulusları vuracak keskin bir kılıç uzanıyor. Onları demir çomakla güdecek. Her Şeye Gücü Yeten Tanrı'nın ateşli gazabının şarabını üreten masarayı kendisi çiğneyecek.
Daga bakinsa takobi mai kaifi ya fito. Da shi zai karkashe al’ummai. “Zai yi mulkinsu da sandan sarautar ƙarfe.” Yana tattake wurin matsin ruwan inabi na fushin Allah Maɗaukaki.
16 Kaftanının ve kalçasının üzerinde şu ad yazılıydı: KRALLARIN KRALI VE RABLERİN RABBİ
A rigarsa da kuma a cinyarsa akwai wannan suna a rubuce, Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji.
17 Bundan sonra güneşte duran bir melek gördüm. Göğün ortasında uçan bütün kuşları yüksek sesle çağırdı: “Kralların, komutanların, güçlü adamların, atlarla binicilerinin, özgür köle, küçük büyük, hepsinin etini yemek için toplanın, Tanrı'nın büyük şölenine gelin!”
Na kuma ga wani mala’ika tsaye a cikin rana, wanda ya yi kira da babbar murya ga dukan tsuntsaye da suke tashi sama a tsakiyar sararin sama cewa, “Ku zo, ku taru don babban bikin nan na Allah,
don ku ci naman sarakuna, jarumawa, da kuma manyan mutane, na dawakai da mahayansu, da kuma naman dukan mutane,’yantacce da bawa, babba da yaro.”
19 Sonra canavarı, dünya krallarını ve onların ordularını, ata binmiş Olan'la O'nun ordusuna karşı savaşmak üzere toplanmış gördüm.
Sa’an nan na ga dabbar da sarakunan duniya da mayaƙansu sun taru don su yi yaƙi da wannan wanda yake kan farin dokin da kuma mayaƙansa.
20 Canavarla onun önünde doğaüstü belirtiler gerçekleştiren sahte peygamber yakalandı. Sahte peygamber, canavarın işaretini alıp heykeline tapanları bu belirtilerle saptırmıştı. Her ikisi de kükürtle yanan ateş gölüne diri diri atıldı. (Limnē Pyr )
Amma aka kama dabbar tare da annabin ƙaryan nan wanda ya aikata alamu masu banmamaki a madadinta. Da waɗannan alamun ne ya ruɗe waɗanda suka sami alamar dabbar suka kuma bauta wa siffarta. Aka jefa dukansu biyu da rai cikin tafkin wuta ta da farar wuta mai ci. (Limnē Pyr )
21 Geriye kalanlar, ata binmiş Olan'ın ağzından uzanan kılıçla öldürüldü. Bütün kuşlar bunların etiyle doydu.
Sauran kuma aka kashe su da takobin da ya fito daga bakin wannan wanda yake kan dokin. Dukan tsuntsaye kuwa suka ci namansu iyakar iyawarsu.