< Vahiy 16 >

1 Sonra tapınaktan yükselen gür bir sesin yedi meleğe, “Gidin, Tanrı'nın öfkesiyle dolu yedi tası yeryüzüne boşaltın!” dediğini işittim.
Sai na ji wata babbar murya daga haikalin tana ce wa mala’iku bakwai nan, “Ku tafi ku zuba kwanoni bakwai nan na fushin Allah a kan duniya.”
2 Birinci melek gidip tasını yeryüzüne boşalttı. Canavarın işaretini taşıyıp heykeline tapanların üzerinde acı veren iğrenç yaralar oluştu.
Mala’ika na fari ya je ya juye kwanonsa a bisan ƙasa, sai munanan gyambuna masu zafi suka fito a jikin mutanen da suke da alamar dabbar suka kuma yi wa siffarta sujada.
3 İkinci melek tasını denize boşalttı. Deniz ölü kanına benzer kana dönüştü, içindeki bütün canlılar öldü.
Mala’ika na biyu ya juye kwanonsa a bisan teku, sai tekun ya zama jini kamar na mataccen mutum, kuma kowane abu mai rai da yake cikin tekun ya mutu.
4 Üçüncü melek tasını ırmaklara, su pınarlarına boşalttı; bunlar da kana dönüştü.
Mala’ika na uku ya juye kwanonsa a bisan koguna da maɓulɓulan ruwa, sai suka zama jini.
5 Sulardan sorumlu meleğin şöyle dediğini işittim: “Var olan, var olmuş olan kutsal Tanrı! Bu yargılarında adilsin.
Sa’an nan na ji mala’ikan da yake lura da ruwaye ya ce, “Kai mai adalci ne cikin waɗannan hukuntai, kai da kake yanzu, kake kuma a dā, Mai Tsarki, saboda yadda ka yi hukuncin nan;
6 Kutsalların ve peygamberlerin kanını döktükleri için, İçecek olarak sen de onlara kan verdin. Bunu hak ettiler.”
gama sun zub da jinin tsarkakanka da kuma annabawanka, ka kuwa ba su jini su sha, yadda ya dace da su.”
7 Sunaktan gelen bir sesin, “Evet, Her Şeye Gücü Yeten Rab Tanrı, Yargıların doğru ve adildir” dediğini işittim.
Na kuma ji bagaden ya amsa, “I, Ubangiji Allah, Maɗaukaki, hukuntanka daidai yake na adalci ne kuma.”
8 Dördüncü melek tasını güneşe boşalttı. Bununla güneşe insanları yakma gücü verildi.
Mala’ika na huɗu ya juye kwanonsa a bisan rana, sai aka ba wa rana iko ta ƙona mutane da wuta.
9 İnsanlar korkunç bir ısıyla kavruldular. Tövbe edip bu belalara egemen olan Tanrı'yı yücelteceklerine, O'nun adına küfrettiler.
Aka ƙone su da zafin wuta mai tsanani suka kuwa la’anci sunan Allah wanda yake da iko a kan waɗannan annoban, amma suka ƙi su tuba su kuma ɗaukaka shi.
10 Beşinci melek tasını canavarın tahtına boşalttı. Canavarın egemenliği karanlığa gömüldü. İnsanlar ıstıraptan dillerini ısırdılar.
Mala’ika na biyar ya juye kwanonsa a bisan gadon sarautar dabbar, mulkinta kuwa ya zama duhu. Mutane suka yi ta cizon bakinsu saboda azaba
11 Istırap ve yaralarından ötürü Göğün Tanrısı'na küfrettiler. Yaptıklarından tövbe etmediler.
suka kuma la’anci Allah na sama saboda zafinsu, da kuma saboda gyambunansu, amma suka ƙi su tuba daga abin da suka riga suka yi.
12 Altıncı melek tasını büyük Fırat Irmağı'na boşalttı. Gündoğusundan gelen kralların yolu açılsın diye ırmağın suları kurudu.
Mala’ika na shida ya juye kwanonsa a bisan babban kogin Yuferites, sai ruwansa ya shanye don a shirya hanya saboda sarakuna daga Gabas.
13 Bundan sonra ejderhanın ağzından, canavarın ağzından ve sahte peygamberin ağzından kurbağaya benzer üç kötü ruhun çıktığını gördüm.
Sa’an nan na ga mugayen ruhohi guda uku da suka yi kamar kwaɗi; suka fito daga bakin macijin nan, da kuma daga bakin dabbar, da kuma daga bakin annabin ƙaryan nan.
14 Bunlar doğaüstü belirtiler gerçekleştiren cinlerin ruhlarıdır. Her Şeye Gücü Yeten Tanrı'nın büyük gününde olacak savaş için bütün dünyanın krallarını toplamaya gidiyorlar.
Su ruhohin aljanu ne da suke aikata abubuwan banmamaki, sukan je wurin sarakunan dukan duniya, don su tattara su don yaƙi a babbar ranar Allah Maɗaukaki.
15 “İşte hırsız gibi geliyorum! Çıplak dolaşmamak ve utanç içinde kalmamak için uyanık durup giysilerini üstünde bulundurana ne mutlu!”
“Ga shi, ina zuwa kamar ɓarawo! Mai albarka ne wanda yake zama a faɗake yana kuma saye da tufafinsa, don kada yă yi tafiya tsirara a kuma kunyata shi.”
16 Üç kötü ruh, kralları İbranice Armagedon denilen yere topladılar.
Sa’an nan aka tattara sarakuna zuwa wurin da a Ibraniyanci ake kira Armageddon.
17 Yedinci melek tasını havaya boşalttı. Tapınaktaki tahttan yükselen gür bir ses, “Tamam!” dedi.
Mala’ika na bakwai ya juye kwanonsa cikin iska, daga haikalin kuwa sai aka ji wata babbar murya daga kursiyin, tana cewa, “An gama!”
18 O anda şimşekler çaktı, uğultular, gök gürlemeleri işitildi. Öyle büyük bir deprem oldu ki, yeryüzünde insan oldu olalı bu kadar büyük bir deprem olmamıştı.
Sai ga walƙiya, ƙararraki, tsawa da kuma matsananciyar girgizar ƙasa. Ba a taɓa yin irin wannan girgizar ƙasar ba, tun kasancewar mutum a duniya, girgizar ƙasar kuwa gawurtacciya ce.
19 Büyük kent üçe bölündü. Ulusların kentleri yerle bir oldu. Tanrı büyük Babil'i anımsadı, ona ateşli gazabının şarabını içeren kâseyi verdi.
Babban birnin ya rabu kashi uku, biranen al’ummai kuma suka rurrushe. Allah ya tuna da Babilon Mai Girma ya kuma ba ta kwaf cike da ruwan inabin fushinsa.
20 Bütün adalar ortadan kalktı, dağlar yok oldu.
Kowane tsibiri ya gudu ba a kuwa ƙara ganin duwatsu ba.
21 İnsanların üzerine gökten tanesi yaklaşık kırk kilo ağırlığında iri dolu yağdı. Dolu belası öyle korkunçtu ki, insanlar bu yüzden Tanrı'ya küfrettiler.
Daga sararin sama manyan ƙanƙara masu nauyin gaske suka fāɗo a kan mutane. Suka kuma la’anci Allah saboda annobar ƙanƙarar, domin annobar ta yi muni ƙwarai.

< Vahiy 16 >