< Mezmurlar 88 >

1 Korahoğulları'nın mezmuru - İlahi - Müzik şefi için - “Mahalat Leannot” makamında - Ezrahlı Heman'ın Maskili Ya RAB, beni kurtaran Tanrı, Gece gündüz sana yakarıyorum.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Duam sana erişsin, Kulak ver yakarışıma.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 Çünkü sıkıntıya doydum, Canım ölüler diyarına yaklaştı. (Sheol h7585)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
4 Ölüm çukuruna inenler arasında sayılıyorum, Tükenmiş gibiyim;
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 Ölüler arasına atılmış, Artık anımsamadığın, İlginden yoksun, Mezarda yatan cesetler gibiyim.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Beni çukurun dibine, Karanlıklara, derinliklere attın.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Öfken üzerime çöktü, Dalga dalga kızgınlığınla beni ezdin. (Sela)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Yakınlarımı benden uzaklaştırdın, İğrenç kıldın beni gözlerinde. Kapalı kaldım, çıkamıyorum.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Üzüntüden gözlerimin feri sönüyor, Her gün sana yakarıyorum, ya RAB, Ellerimi sana açıyorum.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Harikalarını ölülere mi göstereceksin? Ölüler mi kalkıp seni övecek? (Sela)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Sevgin mezarda, Sadakatin yıkım diyarında duyurulur mu?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Karanlıklarda harikaların, Unutulmuşluk diyarında doğruluğun bilinir mi?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Ama ben, ya RAB, yardıma çağırıyorum seni, Sabah duam sana varıyor.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Niçin beni reddediyorsun, ya RAB, Neden yüzünü benden gizliyorsun?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Düşkünüm, gençliğimden beri ölümle burun burunayım, Dehşetlerinin altında tükendim.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Şiddetli gazabın üzerimden geçti, Saçtığın dehşet beni yedi bitirdi.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Bütün gün su gibi kuşattılar beni, Çevremi tümüyle sardılar.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Eşi dostu benden uzaklaştırdın, Tek dostum karanlık kaldı.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.

< Mezmurlar 88 >