< Mezmurlar 72 >

1 Süleyman'ın mezmuru Ey Tanrı, adaletini krala, Doğruluğunu kral oğluna armağan et.
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 Senin halkını doğrulukla, Mazlum kullarını adilce yargılasın!
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 Dağlar, tepeler, Halka adilce gönenç getirsin!
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 Mazlumlara hakkını versin, Yoksulların çocuklarını kurtarsın, Zalimleriyse ezsin!
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 Güneş ve ay durdukça, Kral kuşaklar boyunca yaşasın;
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 Yeni biçilmiş çayıra düşen yağmur gibi, Toprağı sulayan bereketli yağmurlar gibi olsun!
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 Onun günlerinde doğruluk serpilip gelişsin, Ay ışıdığı sürece esenlik artsın!
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 Egemenlik sürsün denizden denize, Fırat'tan yeryüzünün ucuna dek!
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 Çöl kabileleri diz çöksün önünde, Düşmanları toz yalasın.
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 Tarşiş'in ve kıyı ülkelerinin kralları Ona haraç getirsin, Saba ve Seva kralları armağanlar sunsun!
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 Bütün krallar önünde yere kapansın, Bütün uluslar ona kulluk etsin!
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 Çünkü yardım isteyen yoksulu, Dayanağı olmayan düşkünü o kurtarır.
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 Yoksula, düşküne acır, Düşkünlerin canını kurtarır.
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 Baskıdan, zorbalıktan özgür kılar onları, Çünkü onun gözünde onların kanı değerlidir.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 Yaşasın kral! Ona Saba altını versinler; Durmadan dua etsinler onun için, Gün boyu onu övsünler!
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 Ülkede bol buğday olsun, Dağ başlarında dalgalansın! Başakları Lübnan gibi verimli olsun, Kent halkı ot gibi serpilip çoğalsın!
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 Kralın adı sonsuza dek yaşasın, Güneş durdukça adı var olsun, Onun aracılığıyla insanlar kutsansın, Bütün uluslar “Ne mutlu ona” desin!
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 RAB Tanrı'ya, İsrail'in Tanrısı'na övgüler olsun, Harikalar yaratan yalnız O'dur.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 Yüce adına sonsuza dek övgüler olsun, Bütün yeryüzü O'nun yüceliğiyle dolsun! Amin! Amin!
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 İşay oğlu Davut'un duaları burada bitiyor.
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.

< Mezmurlar 72 >