< Mezmurlar 49 >

1 Müzik şefi için - Korahoğulları'nın mezmuru Ey bütün halklar, dinleyin! Kulak verin hepiniz, ey dünyada yaşayanlar,
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
2 Halk çocukları, bey çocukları, Zenginler, yoksullar!
babba da yaro mai arziki da talaka.
3 Bilgelik dökülecek ağzımdan, Anlayış sağlayacak içimdeki düşünceler,
Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
4 Kulak vereceğim özdeyişlere, Lirle yorumlayacağım bilmecemi.
Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
5 Niçin korkayım kötü günlerde Niyeti bozuk düşmanlarım çevremi sarınca?
Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
6 Onlar varlıklarına güvenir, Büyük servetleriyle böbürlenirler.
waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
7 Kimse kimsenin hayatının bedelini ödeyemez, Tanrı'ya fidye veremez.
Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
8 Çünkü hayatın fidyesi büyüktür, Kimse ödemeye yeltenmemeli.
kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
9 Böyle olmasa, Sonsuza dek yaşar insan, Mezar yüzü görmez.
da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
10 Kuşkusuz herkes biliyor bilgelerin öldüğünü, Aptallarla budalaların yok olduğunu. Mallarını başkalarına bırakıyorlar.
Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
11 Mezarları, sonsuza dek evleri, Kuşaklar boyu konutları olacak, Topraklarına kendi adlarını verseler bile.
Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
12 Bütün gösterişine karşın geçicidir insan, Ölüp giden hayvanlar gibi.
Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
13 Budalaların yolu, Onların sözünü onaylayanların sonu budur. (Sela)
Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
14 Sürü gibi ölüler diyarına sürülecekler, Ölüm güdecek onları. Tan ağarınca doğrular onlara egemen olacak, Cesetleri çürüyecek, Ölüler diyarı onlara konut olacak. (Sheol h7585)
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
15 Ama Tanrı beni Ölüler diyarının pençesinden kurtaracak Ve yanına alacak. (Sela) (Sheol h7585)
Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
16 Korkma biri zenginleşirse, Evinin görkemi artarsa.
Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
17 Çünkü ölünce hiçbir şey götüremez, Görkemi onunla mezara gitmez.
gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
18 Yaşarken kendini mutlu saysa bile, Başarılı olunca övülse bile.
Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
19 Atalarının kuşağına katılacak, Onlar ki asla ışık yüzü görmeyecekler.
zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
20 Bütün gösterişine karşın anlayışsızdır insan, Ölüp giden hayvanlar gibi.
Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.

< Mezmurlar 49 >