< Mezmurlar 41 >

1 Müzik şefi için - Davut'un mezmuru Ne mutlu yoksulu düşünene! RAB kurtarır onu kötü günde.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
2 Korur RAB, yaşatır onu, Ülkede mutlu kılar, Terk etmez düşmanlarının eline.
Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
3 Destek olur RAB ona Yatağa düşünce; Hastalandığında sağlığa kavuşturur onu.
Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
4 “Acı bana, ya RAB!” dedim, “Şifa ver bana, çünkü sana karşı günah işledim!”
Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
5 Kötü konuşuyor düşmanlarım ardımdan: “Ne zaman ölecek adı batası?” diyorlar.
Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
6 Biri beni görmeye geldi mi, boş laf ediyor, Fesat topluyor içinde, Sonra dışarı çıkıp fesadı yayıyor.
Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
7 Benden nefret edenlerin hepsi Fısıldaşıyor aralarında bana karşı, Zararımı düşünüyorlar,
Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
8 “Başına öyle kötü bir şey geldi ki” diyorlar, “Yatağından kalkamaz artık.”
“Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
9 Ekmeğimi yiyen, güvendiğim yakın dostum bile İhanet etti bana.
Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
10 Bari sen acı bana, ya RAB, kaldır beni. Bunların hakkından geleyim.
Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
11 Düşmanım zafer çığlığı atmazsa, O zaman anlarım benden hoşnut kaldığını.
Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
12 Dürüstlüğümden ötürü bana destek olur, Sonsuza dek beni huzurunda tutarsın.
Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
13 Öncesizlikten sonsuza dek, Övgüler olsun İsrail'in Tanrısı RAB'be! Amin! Amin!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.

< Mezmurlar 41 >