< Mezmurlar 38 >

1 Anma sunusu için Davut'un mezmuru Ya RAB, öfkelenip azarlama beni, Gazapla yola getirme!
Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 Okların içime saplandı, Elin üzerime indi.
Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
3 Öfken yüzünden sağlığım bozuldu, Günahım yüzünden rahatım kaçtı.
Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
4 Çünkü suçlarım başımdan aştı, Taşınmaz bir yük gibi sırtımda ağırlaştı.
Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
5 Akılsızlığım yüzünden Yaralarım iğrenç, irinli.
Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
6 Eğildim, iki büklüm oldum, Gün boyu yaslı dolaşıyorum.
An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
7 Çünkü belim ateş içinde, Sağlığım bozuk.
Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
8 Tükendim, ezildim alabildiğine, İnliyorum yüreğimin acısından.
Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
9 Ya Rab, bütün özlemlerimi bilirsin, İniltilerim senden gizli değil.
Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
10 Yüreğim çarpıyor, gücüm tükeniyor, Gözlerimin feri bile söndü.
Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
11 Eşim dostum kaçar oldu derdimden, Yakınlarım uzak duruyor benden.
Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
12 Canıma susayanlar bana tuzak kuruyor, Zararımı isteyenler kuyumu kazıyor, Gün boyu hileler düşünüyorlar.
Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
13 Ama ben bir sağır gibi duymuyorum, Bir dilsiz gibi ağzımı açmıyorum;
Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
14 Duymaz, Ağzında yanıt bulunmaz bir adama döndüm.
Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
15 Umudum sende, ya RAB, Sen yanıtlayacaksın, ya Rab, Tanrım benim!
Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
16 Çünkü dua ediyorum: “Halime sevinmesinler, Ayağım kayınca böbürlenmesinler!”
Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
17 Düşmek üzereyim, Acım hep içimde.
Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
18 Suçumu itiraf ediyorum, Günahım yüzünden kaygılanıyorum.
Na furta laifina; na damu da zunubina.
19 Ama düşmanlarım güçlü ve dinç, Yok yere benden nefret edenler çok.
Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
20 İyiliğe karşı kötülük yapanlar bana karşı çıkar, İyiliğin peşinde olduğum için.
Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
21 Beni terk etme, ya RAB! Ey Tanrım, benden uzak durma!
Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
22 Yardımıma koş, Ya Rab, kurtuluşum benim!
Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.

< Mezmurlar 38 >