< Mezmurlar 33 >

1 Ey doğru insanlar, RAB'be sevinçle haykırın! Dürüstlere O'nu övmek yaraşır.
Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
2 Lir çalarak RAB'be şükredin, On telli çenk eşliğinde O'nu ilahilerle övün.
Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
3 O'na yeni bir ezgi söyleyin, Sevinç çığlıklarıyla sazınızı konuşturun.
Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
4 Çünkü RAB'bin sözü doğrudur, Her işi sadakatle yapar.
Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
5 Doğruluğu, adaleti sever, RAB'bin sevgisi yeryüzünü doldurur.
Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
6 Gökler RAB'bin sözüyle, Gök cisimleri ağzından çıkan solukla yaratıldı.
Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
7 Deniz sularını bir araya toplar, Engin suları ambarlara depolar.
Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
8 Bütün yeryüzü RAB'den korksun, Dünyada yaşayan herkes O'na saygı duysun.
Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
9 Çünkü O söyleyince, her şey var oldu; O buyurunca, her şey belirdi.
Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
10 RAB ulusların planlarını bozar, Halkların tasarılarını boşa çıkarır.
Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
11 Ama RAB'bin planları sonsuza dek sürer, Yüreğindeki tasarılar kuşaklar boyunca değişmez.
Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
12 Ne mutlu Tanrısı RAB olan ulusa, Kendisi için seçtiği halka!
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13 RAB göklerden bakar, Bütün insanları görür.
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
14 Oturduğu yerden, Yeryüzünde yaşayan herkesi gözler.
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15 Herkesin yüreğini yaratan, Yaptıkları her şeyi tartan O'dur.
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16 Ne büyük ordularıyla zafer kazanan kral var, Ne de büyük gücüyle kurtulan yiğit.
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17 Zafer için at boş bir umuttur, Büyük gücüne karşın kimseyi kurtaramaz.
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18 Ama RAB'bin gözü kendisinden korkanların, Sevgisine umut bağlayanların üzerindedir;
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19 Böylece onları ölümden kurtarır, Kıtlıkta yaşamalarını sağlar.
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
20 Umudumuz RAB'dedir, Yardımcımız, kalkanımız O'dur.
Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
21 O'nda sevinç bulur yüreğimiz, Çünkü O'nun kutsal adına güveniriz.
A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22 Madem umudumuz sende, Sevgin üzerimizde olsun, ya RAB!
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.

< Mezmurlar 33 >