< Mezmurlar 145 >
1 Davut'un övgü ilahisi Ey Tanrım, ey Kral, seni yücelteceğim, Adını sonsuza dek öveceğim.
Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
2 Seni her gün övecek, Adını sonsuza dek yücelteceğim.
Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
3 RAB büyüktür, yalnız O övgüye yaraşıktır, Akıl ermez büyüklüğüne.
Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
4 Yaptıkların kuşaktan kuşağa şükranla anılacak, Güçlü işlerin duyurulacak.
Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
5 Düşüneceğim harika işlerini, İnsanlar büyüklüğünü, yüce görkemini konuşacak.
Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
6 Yaptığın müthiş işlerin gücünden söz edecekler, Ben de senin büyüklüğünü duyuracağım.
Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
7 Eşsiz iyiliğinin anılarını kutlayacak, Sevinç ezgileriyle övecekler doğruluğunu.
Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
8 RAB lütufkâr ve sevecendir, Tez öfkelenmez, sevgisi engindir.
Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
9 RAB herkese iyi davranır, Sevecenliği bütün yapıtlarını kapsar.
Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
10 Bütün yapıtların sana şükreder, ya RAB, Sadık kulların sana övgüler sunar.
Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
11 Krallığının yüceliğini anlatır, Kudretini konuşur;
Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
12 Herkes senin gücünü, Krallığının yüce görkemini bilsin diye.
saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
13 Senin krallığın ebedi krallıktır, Egemenliğin kuşaklar boyunca sürer. RAB verdiği bütün sözleri tutar, Her davranışı sadıktır.
Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
14 RAB her düşene destek olur, İki büklüm olanları doğrultur.
Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
15 Herkesin umudu sende, Onlara yiyeceklerini zamanında veren sensin.
Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
16 Elini açar, Bütün canlıları doyurursun dilediklerince.
Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
17 RAB bütün davranışlarında adil, Yaptığı bütün işlerde sevecendir.
Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
18 RAB kendisine yakaran, İçtenlikle yakaran herkese yakındır.
Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
19 Dileğini yerine getirir kendisinden korkanların, Feryatlarını işitir, onları kurtarır.
Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
20 RAB korur kendisini seven herkesi, Yok eder kötülerin hepsini.
Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
21 RAB'be övgüler sunsun ağzım! Bütün canlılar O'nun kutsal adına, Sonsuza dek övgüler dizsin.
Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.