< Mezmurlar 139 >

1 Müzik şefi için - Davut'un mezmuru Ya RAB, sınayıp tanıdın beni.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
2 Oturup kalkışımı bilirsin, Niyetimi uzaktan anlarsın.
Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
3 Gittiğim yolu, yattığım yeri inceden inceye elersin, Bütün yaptıklarımdan haberin var.
Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
4 Daha sözü ağzıma almadan, Söyleyeceğim her şeyi bilirsin, ya RAB.
Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
5 Beni çepeçevre kuşattın, Elini üzerime koydun.
Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
6 Kaldıramam böylesi bir bilgiyi, Başa çıkamam, erişemem.
Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
7 Nereye gidebilirim senin Ruhun'dan, Nereye kaçabilirim huzurundan?
Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
8 Göklere çıksam, oradasın, Ölüler diyarına yatak sersem, yine oradasın. (Sheol h7585)
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
9 Seherin kanatlarını alıp uçsam, Denizin ötesine konsam,
In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
10 Orada bile elin yol gösterir bana, Sağ elin tutar beni.
can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
11 Desem ki, “Karanlık beni kaplasın, Çevremdeki aydınlık geceye dönsün.”
In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
12 Karanlık bile karanlık sayılmaz senin için, Gece, gündüz gibi ışıldar, Karanlıkla aydınlık birdir senin için.
duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
13 İç varlığımı sen yarattın, Annemin rahminde beni sen ördün.
Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
14 Sana övgüler sunarım, Çünkü müthiş ve harika yaratılmışım. Ne harika işlerin var! Bunu çok iyi bilirim.
Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
15 Gizli yerde yaratıldığımda, Yerin derinliklerinde örüldüğümde, Bedenim senden gizli değildi.
Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
16 Henüz döl yatağındayken gözlerin gördü beni; Bana ayrılan günlerin hiçbiri gelmeden, Hepsi senin kitabına yazılmıştı.
Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
17 Hakkımdaki düşüncelerin ne değerli, ey Tanrı, Sayıları ne çok!
Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
18 Kum tanelerinden fazladır saymaya kalksam. Uyanıyorum, hâlâ seninleyim.
A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
19 Ey Tanrı, keşke kötüleri öldürsen! Ey eli kanlı insanlar, uzaklaşın benden!
Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
20 Çünkü senin için kötü konuşuyorlar, Adını kötüye kullanıyor düşmanların.
Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
21 Ya RAB, nasıl tiksinmem senden tiksinenlerden? Nasıl iğrenmem sana başkaldıranlardan?
Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
22 Onlardan tümüyle nefret ediyor, Onları düşman sayıyorum.
Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
23 Ey Tanrı, yokla beni, tanı yüreğimi, Sına beni, öğren kaygılarımı.
Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
24 Bak, seni gücendiren bir yönüm var mı, Öncülük et bana sonsuz yaşam yolunda!
Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.

< Mezmurlar 139 >