< Mezmurlar 132 >
1 Hac ilahisi Ya RAB, Davut'un hatırı için, Çektiği bütün zorlukları, Sana nasıl ant içtiğini, Yakup'un güçlü Tanrısı'na adak adadığını anımsa:
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 “Evime gitmeyeceğim, Yatağıma uzanmayacağım,
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 Gözlerime uyku girmeyecek, Göz kapaklarım kapanmayacak,
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 RAB'be bir yer, Yakup'un güçlü Tanrısı'na bir konut buluncaya dek.”
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 Antlaşma Sandığı'nın Efrata'da olduğunu duyduk, Onu Yaar kırlarında bulduk.
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 “RAB'bin konutuna gidelim, Ayağının taburesi önünde tapınalım” dedik.
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 Çık, ya RAB, yaşayacağın yere, Gücünü simgeleyen sandıkla birlikte.
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 Kâhinlerin doğruluğu kuşansın, Sadık kulların sevinç çığlıkları atsın.
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 Kulun Davut'un hatırı için, Meshettiğin krala yüz çevirme.
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 RAB Davut'a kesin ant içti, Andından dönmez: “Senin soyundan birini tahtına oturtacağım.
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 Eğer oğulların antlaşmama, Vereceğim öğütlere uyarlarsa, Onların oğulları da sonsuza dek Senin tahtına oturacak.”
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 Çünkü RAB Siyon'u seçti, Onu konut edinmek istedi.
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 “Sonsuza dek yaşayacağım yer budur” dedi, “Burada oturacağım, çünkü bunu kendim istedim.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 Çok bereketli kılacağım erzağını, Yiyecekle doyuracağım yoksullarını.
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 Kurtuluşla donatacağım kâhinlerini; Hep sevinç ezgileri söyleyecek sadık kulları.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 Burada Davut soyundan güçlü bir kral çıkaracağım, Meshettiğim kralın soyunu Işık olarak sürdüreceğim.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 Düşmanlarını utanca bürüyeceğim, Ama onun başındaki taç parıldayacak.”
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”