< Mezmurlar 116 >
1 RAB'bi seviyorum, Çünkü O feryadımı duyar.
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2 Bana kulak verdiği için, Yaşadığım sürece O'na sesleneceğim.
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
3 Ölüm iplerine dolaşmıştım, Ölüler diyarının kâbusu yakama yapışmıştı, Sıkıntıya, acıya gömülmüştüm. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
4 O zaman RAB'bi adıyla çağırdım, “Aman, ya RAB, kurtar canımı!” dedim.
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
5 RAB lütufkâr ve adildir, Sevecendir Tanrımız.
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6 RAB saf insanları korur, Tükendiğim zaman beni kurtardı.
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
7 Ey canım, yine huzura kavuş, Çünkü RAB sana iyilik etti.
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
8 Sen, ya RAB, canımı ölümden, Gözlerimi yaştan, Ayaklarımı sürçmekten kurtardın.
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
9 Yaşayanların diyarında, RAB'bin huzurunda yürüyeceğim.
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
10 İman ettim, “Büyük acı çekiyorum” dediğim zaman bile.
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
11 Şaşkınlık içinde, “Bütün insanlar yalancı” dedim.
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
12 Ne karşılık verebilirim RAB'be, Bana yaptığı onca iyilik için?
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13 Kurtuluş sunusu olarak kadeh kaldırıp RAB'bi adıyla çağıracağım.
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14 Bütün halkının önünde, RAB'be adadıklarımı yerine getireceğim.
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15 RAB'bin gözünde değerlidir Sadık kullarının ölümü.
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16 Ya RAB, ben gerçekten senin kulunum; Kulun, hizmetçinin oğluyum, Sen çözdün bağlarımı.
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17 Ya RAB, seni adınla çağırıp Şükran kurbanı sunacağım.
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18 RAB'be adadıklarımı yerine getireceğim Bütün halkının önünde,
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19 RAB'bin Tapınağı'nın avlularında, Senin orta yerinde, ey Yeruşalim! RAB'be övgüler sunun!
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.