< Mezmurlar 112 >

1 Övgüler sunun RAB'be! Ne mutlu RAB'den korkan insana, O'nun buyruklarından büyük zevk alana!
Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
2 Soyu yeryüzünde güç kazanacak, Doğruların kuşağı kutsanacak.
’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
3 Bolluk ve zenginlik eksilmez evinden, Sonsuza dek sürer doğruluğu.
Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
4 Karanlıkta ışık doğar dürüstler için, Lütfeden, sevecen, doğru insanlar için.
Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
5 Ne mutlu eli açık olan, ödünç veren, İşlerini adaletle yürüten insana!
Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
6 Asla sarsılmaz, Sonsuza dek anılır doğru insan.
Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
7 Kötü haberden korkmaz, Yüreği sarsılmaz, RAB'be güvenir.
Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
8 Gözü pektir, korku nedir bilmez, Sonunda düşmanlarının yenilgisini görür.
Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
9 Armağanlar dağıttı, yoksullara verdi; Doğruluğu sonsuza dek kalıcıdır, Gücü ve saygınlığı artar.
Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
10 Kötü kişi bunu görünce kudurur, Dişlerini gıcırdatır, kendi kendini yer, bitirir. Kötülerin dileği boşa çıkar.
Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.

< Mezmurlar 112 >