< Mezmurlar 109 >

1 Müzik şefi için - Davut'un mezmuru Ey övgüler sunduğum Tanrı, Sessiz kalma!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 Çünkü kötüler, yalancılar Bana karşı ağzını açtı, Karalıyorlar beni.
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 Nefret dolu sözlerle beni kuşatıp Yok yere bana savaş açtılar.
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 Sevgime karşılık bana düşman oldular, Bense dua etmekteyim.
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 İyiliğime kötülük, Sevgime nefretle karşılık verdiler.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Kötü bir adam koy düşmanın başına, Sağında onu suçlayan biri dursun!
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 Yargılanınca suçlu çıksın, Duası bile günah sayılsın!
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 Ömrü kısa olsun, Görevini bir başkası üstlensin!
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 Çocukları öksüz, Karısı dul kalsın!
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 Çocukları avare gezip dilensin, Yıkık evlerinden uzakta yiyecek arasın!
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 Bütün malları tefecinin ağına düşsün, Emeğini yabancılar yağmalasın!
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 Kimse ona sevgi göstermesin, Öksüzlerine acıyan olmasın!
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 Soyu kurusun, Bir kuşak sonra adı silinsin!
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 Atalarının suçları RAB'bin önünde anılsın, Annesinin günahı silinmesin!
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 Günahları hep RAB'bin önünde dursun, RAB anılarını yok etsin yeryüzünden!
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 Çünkü düşmanım sevgi göstermeyi düşünmedi, Ölesiye baskı yaptı mazluma, yoksula, Yüreği kırık insana.
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 Sevdiği lanet başına gelsin! Madem kutsamaktan hoşlanmıyor, Uzak olsun ondan kutsamak!
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 Laneti bir giysi gibi giydi, Su gibi içine, yağ gibi kemiklerine işlesin lanet!
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 Bir giysi gibi onu örtünsün, Bir kuşak gibi hep onu sarsın!
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Düşmanlarıma, beni kötüleyenlere, RAB böyle karşılık versin!
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 Ama sen, ey Egemen RAB, Adın uğruna bana ilgi göster; Kurtar beni, iyiliğin, sevgin uğruna!
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Çünkü düşkün ve yoksulum, Yüreğim yaralı içimde.
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 Batan güneş gibi geçip gidiyorum, Çekirge gibi silkilip atılıyorum.
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 Dizlerim titriyor oruç tutmaktan; Bir deri bir kemiğe döndüm.
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 Düşmanlarıma yüzkarası oldum; Beni görünce kafalarını sallıyorlar!
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Yardım et bana, ya RAB Tanrım; Kurtar beni sevgin uğruna!
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 Bilsinler bu işte senin elin olduğunu, Bunu senin yaptığını, ya RAB!
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 Varsın lanet etsin onlar, sen kutsa beni, Bana saldıranlar utanacak, Ben kulunsa sevineceğim.
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 Rezilliğe bürünsün beni suçlayanlar, Kaftan giyer gibi utançlarıyla örtünsünler!
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 RAB'be çok şükredeceğim, Kalabalığın arasında O'na övgüler dizeceğim;
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 Çünkü O yoksulun sağında durur, Onu yargılayanlardan kurtarmak için.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.

< Mezmurlar 109 >