< Mezmurlar 102 >

1 Zayıf düşünce derdini RAB'be döken mazlumun duası Ya RAB, duamı işit, Yakarışım sana erişsin.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Sıkıntılı günümde yüzünü benden gizleme, Kulak ver sesime, Seslenince yanıt ver bana hemen.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Çünkü günlerim duman gibi yok oluyor, Kemiklerim ateş gibi yanıyor.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Yüreğim kırgın yemiş ot gibi kurudu, Ekmek yemeyi bile unuttum.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Bir deri bir kemiğe döndüm Acı acı inlemekten.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Issız yerlerdeki ishakkuşunu andırıyorum, Viranelerdeki kukumav gibiyim.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 Gözüme uyku girmiyor, Damda yalnız kalmış bir kuş gibiyim.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Düşmanlarım bütün gün bana hakaret ediyor, Bana dil uzatanlar adımı lanet için kullanıyor.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 Kızıp öfkelendiğin için Külü ekmek gibi yiyor, İçeceğime gözyaşı katıyorum. Beni kaldırıp bir yana attın.
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Günlerim akşam uzayan gölge gibi yitmekte, Ot gibi sararmaktayım.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 Ama sen, sonsuza dek tahtında oturursun, ya RAB, Ünün kuşaklar boyu sürer.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Kalkıp Siyon'a sevecenlik göstereceksin, Çünkü onu kayırmanın zamanıdır, beklenen zaman geldi.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Kulların onun taşlarından hoşlanır, Tozunu bile severler.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Uluslar RAB'bin adından, Yeryüzü kralları görkeminden korkacak.
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 Çünkü RAB Siyon'u yeniden kuracak, Görkem içinde görünecek.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 Yoksulların duasına kulak verecek, Yalvarışlarını asla hor görmeyecek.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Bunlar gelecek kuşak için yazılsın, Öyle ki, henüz doğmamış insanlar RAB'be övgüler sunsun.
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 RAB yücelerdeki kutsal katından aşağı baktı, Göklerden yeryüzünü gözetledi,
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 Tutsakların iniltisini duymak, Ölüm mahkûmlarını kurtarmak için.
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 Böylece halklar ve krallıklar RAB'be tapınmak için toplanınca, O'nun adı Siyon'da, Övgüsü Yeruşalim'de duyurulacak.
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 RAB gücümü kırdı yaşam yolunda, Ömrümü kısalttı.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 “Ey Tanrım, ömrümün ortasında canımı alma!” dedim. “Senin yılların kuşaklar boyu sürer!
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 “Çok önceden attın dünyanın temellerini, Gökler de senin ellerinin yapıtıdır.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Onlar yok olacak, ama sen kalıcısın. Hepsi bir giysi gibi eskiyecek. Onları bir kaftan gibi değiştireceksin, Geçip gidecekler.
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 Ama sen hep aynısın, Yılların tükenmeyecek.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Gözetiminde yaşayacak kullarının çocukları, Senin önünde duracak soyları.”
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< Mezmurlar 102 >