< Süleyman'In Özdeyişleri 6 >
1 Oğlum, eğer birine kefil oldunsa, Onun borcunu yüklendinse,
Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
2 Düştünse tuzağa kendi sözlerinle, Ağzının sözleriyle yakalandınsa,
in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
3 O kişinin eline düştün demektir. Oğlum, şunu yap ve kendini kurtar: Git, yere kapan onun önünde, Ona yalvar yakar.
to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
4 Gözlerine uyku girmesin, Ağırlaşmasın göz kapakların.
Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
5 Avcının elinden ceylan gibi, Kuşbazın elinden kuş gibi kurtar kendini.
Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
6 Ey tembel kişi, git, karıncalara bak, Onların yaşamından bilgelik öğren.
Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
7 Başkanları, önderleri ya da yöneticileri olmadığı halde,
Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
8 Yazın erzaklarını biriktirirler, Yiyeceklerini toplarlar biçim mevsiminde.
duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
9 Ne zamana dek yatacaksın, ey tembel kişi? Ne zaman kalkacaksın uykundan?
Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
10 “Biraz kestireyim, biraz uyuklayayım, Ellerimi kavuşturup şöyle bir uyuyayım” demeye kalmadan,
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
11 Yokluk bir haydut gibi, Yoksulluk bir akıncı gibi gelir üzerine.
talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
12 Ağzında yalanla dolaşan kişi, Soysuz ve fesatçıdır.
Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
13 Göz kırpar, bir sürü ayak oyunu, El kol hareketleri yapar,
wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
14 Ahlaksız yüreğinde kötülük tasarlar, Çekişmeler yaratır durmadan.
wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
15 Bu yüzden ansızın yıkıma uğrayacak, Birdenbire çaresizce yok olacak.
Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
16 RAB'bin nefret ettiği altı şey, İğrendiği yedi şey vardır:
Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
17 Gururlu gözler, Yalancı dil, Suçsuz kanı döken eller,
duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
18 Düzenbaz yürek, Kötülüğe seğirten ayaklar,
zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
19 Yalan soluyan yalancı tanık Ve kardeşler arasında çekişme yaratan kişi.
mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
20 Oğlum, babanın buyruklarına uy, Annenin öğrettiklerinden ayrılma.
Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
21 Bunlar sürekli yüreğinin bağı olsun, Tak onları boynuna.
Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
22 Yolunda sana rehber olacak, Seni koruyacaklar yattığın zaman; Söyleşecekler seninle uyandığında.
Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
23 Bu buyruklar sana çıra, Öğretilenler ışıktır. Eğitici uyarılar yaşam yolunu gösterir.
Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
24 Seni kötü kadından, Başka birinin karısının yaltaklanan dilinden Koruyacak olan bunlardır.
suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
25 Böyle kadınların güzelliği seni ayartmasın, Bakışları seni tutsak etmesin.
Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
26 Çünkü fahişe yüzünden insan bir lokma ekmeğe muhtaç kalır, Başkasının karısıyla yatmak da kişinin canına mal olur.
Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
27 İnsan koynuna ateş alır da, Giysisi yanmaz mı?
Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
28 Korlar üzerinde yürür de, Ayakları kavrulmaz mı?
Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
29 Başkasının karısıyla yatan adamın durumu budur. Böyle bir ilişkiye giren cezasız kalmaz.
Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
30 Aç hırsız karnını doyurmak için çalıyorsa, Kimse onu hor görmez.
Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
31 Ama yakalanırsa, çaldığının yedi katını ödemek zorunda; Varını yoğunu vermek anlamına gelse bile.
Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
32 Zina eden adam sağduyudan yoksundur. Yaptıklarıyla kendini yok eder.
Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
33 Payına düşen dayak ve onursuzluktur, Asla kurtulamaz utançtan.
Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
34 Çünkü kıskançlık kocanın öfkesini azdırır, Öç alırken acımasız olur.
Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
35 Hiçbir fidye kabul etmez, Gönlünü alamazsın armağanların çokluğuyla.
Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.