< Süleyman'In Özdeyişleri 28 >
1 Kötü kişi kendisini kovalayan olmasa bile kaçar, Doğrularsa genç aslan gibi yüreklidir.
Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
2 Ayaklanan ülke çok başlı olur, Ama akıllı, bilgili kişi düzeni sağlar.
Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
3 Yoksulu ezen yoksul, Ürünü harap eden sağanak yağmur gibidir.
Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
4 Yasayı terk eden kötüyü över, Yerine getirense kötüye karşı çıkar.
Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
5 Kötüler adaletten anlamaz, RAB'be yönelenlerse her yönüyle anlar.
Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
6 Dürüst bir yoksul olmak, Yolsuzlukla zengin olmaktan yeğdir.
Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
7 Kutsal Yasa'yı yerine getiren çocuk akıllıdır, Oburlarla arkadaşlık edense babasını utandırır.
Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
8 Faiz ve tefecilikle malına mal katan kişi, Bunu yoksullara acıyan için biriktirir.
Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
9 Yasaya kulağını tıkayanın Duası da iğrençtir.
In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
10 Dürüst kişileri kötü yola saptıran Kendi kazdığı çukura düşer. İyiliği, özü sözü bir olanlar miras alacak.
Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
11 Zengin kendini bilge sanır, Ama akıllı yoksul onun içini okur.
Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
12 Doğruların zaferi coşkuyla kutlanır, Ama kötüler egemen olunca insan kaçacak yer arar.
Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
13 Günahlarını gizleyen başarılı olmaz, İtiraf edip bırakansa merhamet bulur.
Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
14 Günahtan çekinen ne mutludur! İnatçılık edense belaya düşer.
Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
15 Yoksul halkı yöneten kötü kişi Kükreyen aslan, saldırgan ayı gibidir.
Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
16 Gaddar önderin aklı kıttır; Haksız kazançtan nefret edense uzun ömürlü olur.
Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
17 Adam öldürmekten vicdan azabı çeken, mezara dek kaçacaktır; Kimse ona yardım etmesin.
Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
18 Alnı ak yaşayan kurtulur, Yolsuzluk yapan ansızın yıkıma uğrar.
Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
19 Toprağını işleyenin ekmeği bol olur, Hayal peşinde koşansa yoksulluğa doyar.
Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
20 Güvenilir kişi bolluğa erer, Zengin olmaya can atansa beladan kurtulamaz.
Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
21 Hatır gözetmek iyi değildir, Çünkü insan bir lokma ekmek için bile suç işler.
Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
22 Cimri servet peşinde koşar, Yoksulluğa uğrayacağını düşünmez.
Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
23 Başkasını azarlayan sonunda Pohpohlayandan daha çok beğeni kazanır.
Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
24 Annesini ya da babasını soymayı günah saymayan, Haydutla birdir.
Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
25 Açgözlü kavga çıkarır, RAB'be güvenense bolluk içinde yaşar.
Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
26 Kendine güvenen akılsızdır, Bilgece davranan güvenlikte olur.
Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
27 Yoksula verenin eksiği olmaz, Yoksulu görmezden gelense bir sürü lanete uğrar.
Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
28 Kötüler egemen olunca insan kaçacak yer arar, Ama kötüler yok olunca doğrular çoğalır.
Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.