< Süleyman'In Özdeyişleri 18 >

1 Geçimsiz kişi kendi çıkarı peşindedir, İyi öğüde hep karşı çıkar.
Mutumin da ba ya abokantaka yakan nema ya cika burinsa ne kaɗai; yakan ƙi yarda da kowace maganar da take daidai.
2 Akılsız kişi bir şey anlamaktan çok Kendi düşüncelerini açmaktan hoşlanır.
Wawa ba ya sha’awa ya sami fahimta amma abin da yake so ya yi kaɗai, shi ne ya ba da ra’ayinsa.
3 Kötülüğü aşağılanma, Ayıbı utanç izler.
Sa’ad da mugunci ya zo, reni ma kan zo, haka kuma sa’ad da kunya ta zo, shan kunya kan biyo.
4 Bilge kişinin ağzından çıkan sözler derin sular gibidir, Bilgelik pınarı da coşkun bir akarsu.
Kalmomin bakin mutum suna da zurfi kamar ruwaye, amma maɓulɓulan hikima rafi ne mai gudu.
5 Kötüyü kayırmak da, Suçsuzdan adaleti esirgemek de iyi değildir.
Ba shi da kyau ka yi wa mugu alheri ko ka hana wa marar laifi adalci.
6 Akılsızın dudakları çekişmeye yol açar, Ağzı da dayağı davet eder.
Leɓunan wawa kan jawo masa faɗa, bakinsa kuma kan gayyaci dūka.
7 Akılsızın ağzı kendisini mahveder, Dudakları da canına tuzaktır.
Bakin wawa lalatar da kansa yake yi leɓunansa kuma tarko ne ga ransa.
8 Dedikodu tatlı lokma gibidir, İnsanın ta içine işler.
Kalmomin mai gulma kamar abinci mai daɗi suke; sukan gangara zuwa can cikin gaɓoɓin mutum.
9 İşini savsaklayan kişi Yıkıcıya kardeştir.
Wanda yake ragwanci a aikinsa ɗan’uwa ne ga wanda yakan lalatar da abubuwa.
10 RAB'bin adı güçlü kuledir, Ona sığınan doğru kişi için korunaktır.
Sunan Ubangiji hasumiya ce mai ƙarfi; masu adalci kan gudu zuwa wurinta don su zauna lafiya.
11 Zengin servetini bir kale, Aşılmaz bir sur sanır.
Dukiyar masu arziki ita ce birninsu mai katanga; suna gani cewa ba za a iya huda katangar ba.
12 Yürekteki gururu düşüş, Alçakgönüllülüğü ise onur izler.
Kafin fāɗuwarsa zuciyar mutum takan yi girman kai, amma sauƙinkai kan zo kafin girmamawa.
13 Dinlemeden yanıt vermek Ahmaklık ve utançtır.
Duk wanda yakan ba da amsa kafin ya saurara, wannan wauta ce da kuma abin kunya.
14 İnsanın ruhu hastalıkta ona destektir. Ama ezik ruh nasıl dayanabilir?
Sa rai da mutum ke yi kan taimake shi sa’ad da yake ciwo, amma in ya karai, to, tasa ta ƙare.
15 Akıllı kişi bilgiyi satın alır, Bilgenin kulağı da bilgi peşindedir.
Zuciya mai la’akari kan nemi sani; kunnuwan mai hikima kan bincika don yă koya.
16 Armağan, verenin yolunu açar Ve kendisini büyüklerin önüne çıkartır.
Kyauta kan buɗe hanya wa mai bayarwa yakan kuma kai shi a gaban babban mutum.
17 Duruşmada ilk konuşan haklı görünür, Başkası çıkıp onu sorgulayana dek.
Wanda ya fara mai da jawabi yakan zama kamar shi ne mai gaskiya, sai wani ya fito ya yi masa tambaya tukuna.
18 Kura çekişmeleri sona erdirir, Güçlü rakipleri uzlaştırır.
Jefa ƙuri’a kan daidaita tsakanin masu faɗa ta kuma ajiye masu faɗan a rabe.
19 Gücenmiş kardeş surlu kentten daha zor elde edilir. Çekişme sürgülü kale kapısı gibidir.
Ɗan’uwan da aka yi wa laifi ya fi birni mai katanga wuyan shiryawa, kuma faɗace-faɗace suna kama da ƙofofin ƙarfe na fada.
20 İnsanın karnı ağzının meyvesiyle, Dudaklarının ürünüyle doyar.
Daga abin da baki ya furta ne cikin mutum kan cika; girbi daga leɓunansa kuma yakan ƙoshi.
21 Dil ölüme de götürebilir, yaşama da; Konuşmayı seven, dilin meyvesine katlanmak zorundadır.
Harshe yana da ikon rai da mutuwa, kuma waɗanda suke ƙaunarsa za su ci amfaninsa.
22 İyi bir eş bulan iyilik bulur Ve RAB'bin lütfuna erer.
Duk wanda ya sami mace ya sami abu mai kyau ya kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
23 Yoksul acınma dilenir, Zenginin yanıtıysa serttir.
Matalauci kan yi roƙo da taushi, amma mawadaci kan amsa da kakkausar murya.
24 Yıkıma götüren dostlar vardır, Ama öyle dost var ki, kardeşten yakındır insana.
Mutum mai abokai masu yawa kan lalace, amma akwai abokin da yakan manne kurkusa fiye da ɗan’uwa.

< Süleyman'In Özdeyişleri 18 >